Sunday 9 December 2018

ANYI WALKIYA NA M. JABO & MAMAN
TWINS COMPLETE.
By Hauwa jabo
????AN YI WALK'IYA 1-3????

©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NHW

Da gudu take hawa kan matattakalar benen,
kamar zata fad'i, tana k'wala kiran "Mummy!
Mummy!!" da sauri Mumyn ta fito daga wani
d'aki, tana cewa"lafiya?? Arfat irin wannan kira
haka! sai ka ce wadda ta yi gamo?."
A jiyar zuciya ta sauke, tare da k'ank'ame
Mummy, sannan cikin shagwaba tace " Mummy
ba yaya Abeed ba ne ya biyo ni, wai sai ya
dakeni," "Duka! Ai ko ruwan sama bazai dakar
min ke ba bare shi, wai ma to me kika masa da
zai dake kin?"
Arfat na shirin magana ya k'araso gurin yana
fadin"Yauwa Mum mik'o min ita, Allah yarinyar
nan yau sai na 6a66allata a gidannan, don
akanki zan huce haushi ". Ya k'arashe maganar
yana k'ok'arin janyota daga jikin Mum.
Mummy tace"Nak'i na mik'o ta, kaji yaro, amma
bakada ma kunya, ai ko mutuwa na kunyar idon
mahaifi, yarinya har bayan mamanta ta b'uya
kana a mik'ota, sai kace wata y'arka, wai kai
me yake damunka ne Abeed?
Mai ya faru kake neman 6a66alamin yarinya
haka,?" Abeed yace "Mum yarinyar nan tana
zubar min da class Wallahi,ke kuma kina wani
kakkare mata," ya fad'a yana wani yarfee
hannuwa, yana juya jikinsa irin dai yanda
hadaddun guyz sukeyi d'innan "Mum wata
nataciyyar yarinya ce ta lik'a min, ita kuma ta
wani mak'alemun, kamar mayya haka take, Allah
Mum tafi gum mannewa, kuma duk adalilin
Arfat" ya fada yana nunata da yatsa yana
hararanta, "don k'awarta ce, ita ta ba ta
numberta, kuma ko Mum? Ba irin wulak'ancin da
ban mata ba, amma ta k'i daina kirana dan naci
irin nata"
Mummy tace" haba Abeed ina laifin wanda yace
yana sonka ? Yanzu dan Allah akan haka za ka
dakar min yarinya, tanason ta had'a sunnar
Annabi kai kuma kana shirme, to in gaya maka
ban yarda ba."
Arfat da ta la6e bayan Mum tace " Mum kuma
ba ki ganta ba, Allah ta hadu na k'arshe bakiga
yanda take yarfa gayuba"
Danllah rufee ma mutane baki, ya ja dogon
tsaki, "had'uwarta ta banza, ke wai yaushe zaki
gane cewa yanzu komai saida Coins ake yinsa,?
Yanzu gaya mun waye babanta a k'asar nan.?
'yar gidan malam Shehu da ita ta zo tana
damuna kawai".
Mummy murmushi kawai ta yi, dan tasan
k'arshen zancen kenan yace talakace, " Talaka
bawan Allah nidai M. jabo da M. Twins munsan
cewa talauci daga Allah ne, haka dukiya ma
daga Allah, mafi d'aukaka da soyuwa a gurin
Allah shine maki tak'wa a cikin bayin Allah "
Mum kam idan da sabo ta riga ta saba da halin
Abeed, tun bai kai haka ba, halinsa ke nan tun
yana yaro, tun tana ganin kamar k'uruciya ne,
har yazo ya girma bai daina ba, yanzu kam har
ta daina tunanin yarinta ne, don shekarunsa ya
wuce a kira shi da k'aramin yaro.!
"Dallah b'ace mun da gani, kamin na k'araso na
makeka kamin ka maketa a gun," yayi gwafa, ya
gangaro yana guna guni, "ke kuma idan na
kamaki I will show u."
************
Alhaji Bashir Nasari, shine cikakken sunan
mahaifinsu, haifaffen garin kano, kuma
hamshak'in d'an kasuwa ne, yana da arzik'i
sosai don yana d'aya daga cikin manyan 'yan
kasuwa a jahar kano.
Matarshi d'aya Hajiya Maryam, wadda suke kira
Mummy.
Allah ya azzurtashi da yaransa uku Muhammad
da ake kira da Abeed, sai Arfat sai kuma Afrat.
Gida ne wanda mamallakan sa suka gina cikin
so da k'aunar juna, ga ilimi dai_dai gwargwado
suna da tarbiyya.
Sai dai Abeed ya fita daban, akwai girman kai
da Jin shi wata tsiya ne, uwa uba rashin ganin
talaka da gashi, don shi duk abinda zai had'ashi
da talaka baya son shi kwata_kwata a
rayuwarsa
Don haka ya k'udiri niyyar shi ba zai yi aure ba
sai 'yar wani babban mai kud'i a k'asar nan ko a
duniya baki d'aya.
Duk da iyayenshi suna nuna masa illar hakan
amma ba abunda ya chanza daga halinsa.....
Www.jabohauwa.WordPress. com
Www.hauwajabo.blogspot.com
M Twins ?? Auntie M. jabo??
[4/11, 2:54 PM] ????AN YI WALK'IYA 4&5
????
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Misalin 8:30AM, ya fito cikin shirinsa na zuwa
office, saboda shine MD. na babban companyn
Daddy dinsu, dake sharad'a phase 2.
Direct dinning area ya nufa, da nufin yin
breakfast, karaf idonsa akan ladi, ya hango ta
(d'aya daga cikin masu aikinsu) ta gifta ta
wurin dinning table d'in, hakan shi ya tilasta
masa tsayawa tare da k'wala mata kira, jiki na
rawa ta k'arasa inda yake tace"ga ni yalla6ai " "
ke wai wani irin kunnen k'ashi ne da ke ? Eh?
Sau nawa zan ce dake idan an kawo mun abinci
kada ki kuma zuwa ko hanyar da aka bi aka
wuce da abincin, bare kuma kusa da shi"? cikin
rawar murya tace "don Allah ka yi hak'uri, akasi
aka samu yallab'ai, naga har takwas da rabi na
d'auka ka tafi ohis, shiyasa amma ba da niyyar
zu....... " ya katseta tare da fad'in "shut up!
tashi ki ba ni wuri 'yar sa'ido kawai, har an san
lokacin da nake fita da kuma lokacin da nake
dawowa, munafukai 'yan sa ido"jiki a sa6ule ta
mik'e ta fice daga parlourn.
Wani wawan tsaki yaja, sannan ya juya a
yangace ya hau kiran Afrat , da d'an hanzarinta
ta fito daga d'akinsu tace"ga ni yaya"
Abeed yace "waye ya yi girkin can ?" tare da
nuna mata da hannu, tace" haba sai ka tambayi
wanda ya maka girki, ni na yi mana" ya harareta
"ke banason rashin kunya kinaji, are you sure ke
kikayi,?" Kamar ba zata amsaba chan ta ta
gyad'a kai tare da cewa "Im pretty sure".
Yace "kin dai san halina duk ranar da ku ka
sake ku ka bawa 'yan aiki girkina sai kun
gayawa aya zak'inta, tace" haba yaya ai ba ma
ba su, ni ko Arfat muke yi, "gud kya iya tafiya",
ta wuce aranta tace "sau nawa kana lamushe
girkin yan aiki, har kana santi, wane mara aikin
ne zai zaman tashi tunda asuba yana maka girki,
sai kace wasu matanka," ta wuce d'akinsu, ya
zauna ya yakuci wannan ya tsikari wanchan, duk
jarabarshi baya iya chin abinci sosai, ya k'are ya
wucee office...
******
Misalin k'arfe12 na rana Mubarak babban abokin
Abeed ya kai masa ziyara a office d'in sa, bayan
sun gaisa yake sanar da shi zancen dinner da za
a yi na auren abokinsu Jabir.
Sannan ya k'ara da cewa "please Abeed ka yi
k'ok'arin attending, don nasan halinka yanzu za
ka fara kawo mun k'abli cikin ba'adi"
Sai da ya d'aga hannayensa ya watsar alamar
ko oho,!, Sannan ya ce " alright yanzu gaya
mun venue da time na ji idan zan iya zuwa
gurin",murmushi Mubarak ya yi yace "za ma ka
iya zuwa wurin, don ba 6oyayyen guri ba ne".
Abeed yace"No my man, ba abin da nake nufi ba
kenan , I mean gurin ya yi had'uwar da kamar
irina zai je wurin ko kuwa"?
Mubarak hannunsa ya d'auka ya d'ora kan
goshinsa yace "oh! Abeed ka na ba ni mamaki
wallahi, wai mai......." hannu Abeed ya d'aga
masa alamar ya saurara haka.
Sannan yace"just answer my question "
Mubarak yace" ok, a golden Dragon ne". Almost
5 minutes bai ce komai ba, har Mubarak ya gaji
da shirun yace"ya dai?
ba ka ce komai ba ". Sannan Abeed ya yamutsa
fuska, wanda ya k'ara bayyanar da kyansa, a fili,
"gaskiya ba zan je ba ne cox wurin bai mun ba!".
Mubarak ye zaro ido cike da mamaki, "yanzu
Abeed golden Dragon ne bai maka ba?" Kai ya
gyad'a alamar Eh..
Mubarak yayi murmushi, dan yasan Abeed saida
rarrashi, ya cigaba da cewa "gaskiya my man
idan ka yiwa Jabir haka ba zai ji dad'i ba"
Abeed yace"ban yi don na 6ata ransa ba, zan
masa waya ma na bashi hak'uri, bana son zuwa
guri ne na tarar da tarkacen mutane marasa aji
a gurin, wannan ne kawai badan wannan ba
zanje mana" "amma ai ka san waye Jabir! kuma
ka San waye mahaifinsa a garin nan, so bana
tunanin za'ayi k'aranta a gurin, ka sa ni ma ko
ka had'u da wata 'yar minister acan ya fad'a
yana murmushi.
Ya tsine fuska Abeed ya yi, yace" ' ya'yan
ministers ai suna suka tana, kamar 'yar k'
aramin minister mai zan yi da ita" shi dai
Mubarak ido kawai ya zuba yana kallonsa domin
al'amarin Abeed ya girmi tunaninsa, da k'yar ya
samu ya lalla6ashi ya amince akan zai je.
Muje zuwa muji mizai faru a gun.......
Www.hauwajabo.blogspot.com
Www.jabohauwa.WordPress.com
M Twins?? & Auntie M. Jabo ??
[4/11, 2:54 PM] Wacce Zamuyi Book: ????
AN YI WALK'IYA 4&5????
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Misalin 8:30AM, ya fito cikin shirinsa na zuwa
office, saboda shine MD. na babban companyn
Daddy dinsu, dake sharad'a phase 2.
Direct dinning area ya nufa, da nufin yin
breakfast, karaf idonsa akan ladi, ya hango ta
(d'aya daga cikin masu aikinsu) ta gifta ta
wurin dinning table d'in, hakan shi ya tilasta
masa tsayawa tare da k'wala mata kira, jiki na
rawa ta k'arasa inda yake tace"ga ni yalla6ai " "
ke wai wani irin kunnen k'ashi ne da ke ? Eh?
Sau nawa zan ce dake idan an kawo mun abinci
kada ki kuma zuwa ko hanyar da aka bi aka
wuce da abincin, bare kuma kusa da shi"? cikin
rawar murya tace "don Allah ka yi hak'uri, akasi
aka samu yallab'ai, naga har takwas da rabi na
d'auka ka tafi ohis, shiyasa amma ba da niyyar
zu....... " ya katseta tare da fad'in "shut up!
tashi ki ba ni wuri 'yar sa'ido kawai, har an san
lokacin da nake fita da kuma lokacin da nake
dawowa, munafukai 'yan sa ido"jiki a sa6ule ta
mik'e ta fice daga parlourn.
Wani wawan tsaki yaja, sannan ya juya a
yangace ya hau kiran Afrat , da d'an hanzarinta
ta fito daga d'akinsu tace"ga ni yaya"
Abeed yace "waye ya yi girkin can ?" tare da
nuna mata da hannu, tace" haba sai ka tambayi
wanda ya maka girki, ni na yi mana" ya harareta
"ke banason rashin kunya kinaji, are you sure ke
kikayi,?" Kamar ba zata amsaba chan ta ta
gyad'a kai tare da cewa "Im pretty sure".
Yace "kin dai san halina duk ranar da ku ka
sake ku ka bawa 'yan aiki girkina sai kun
gayawa aya zak'inta, tace" haba yaya ai ba ma
ba su, ni ko Arfat muke yi, "gud kya iya tafiya",
ta wuce aranta tace "sau nawa kana lamushe
girkin yan aiki, har kana santi, wane mara aikin
ne zai zaman tashi tunda asuba yana maka girki,
sai kace wasu matanka," ta wuce d'akinsu, ya
zauna ya yakuci wannan ya tsikari wanchan, duk
jarabarshi baya iya chin abinci sosai, ya k'are ya
wucee office...
******
Misalin k'arfe12 na rana Mubarak babban abokin
Abeed ya kai masa ziyara a office d'in sa, bayan
sun gaisa yake sanar da shi zancen dinner da za
a yi na auren abokinsu Jabir.
Sannan ya k'ara da cewa "please Abeed ka yi
k'ok'arin attending, don nasan halinka yanzu za
ka fara kawo mun k'abli cikin ba'adi"
Sai da ya d'aga hannayensa ya watsar alamar
ko oho,!, Sannan ya ce " alright yanzu gaya
mun venue da time na ji idan zan iya zuwa
gurin",murmushi Mubarak ya yi yace "za ma ka
iya zuwa wurin, don ba 6oyayyen guri ba ne".
Abeed yace"No my man, ba abin da nake nufi ba
kenan , I mean gurin ya yi had'uwar da kamar
irina zai je wurin ko kuwa"?
Mubarak hannunsa ya d'auka ya d'ora kan
goshinsa yace "oh! Abeed ka na ba ni mamaki
wallahi, wai mai......." hannu Abeed ya d'aga
masa alamar ya saurara haka.
Sannan yace"just answer my question "
Mubarak yace" ok, a golden Dragon ne". Almost
5 minutes bai ce komai ba, har Mubarak ya gaji
da shirun yace"ya dai?
ba ka ce komai ba ". Sannan Abeed ya yamutsa
fuska, wanda ya k'ara bayyanar da kyansa, a fili,
"gaskiya ba zan je ba ne cox wurin bai mun ba!".
Mubarak ye zaro ido cike da mamaki, "yanzu
Abeed golden Dragon ne bai maka ba?" Kai ya
gyad'a alamar Eh..
Mubarak yayi murmushi, dan yasan Abeed saida
rarrashi, ya cigaba da cewa "gaskiya my man
idan ka yiwa Jabir haka ba zai ji dad'i ba"
Abeed yace"ban yi don na 6ata ransa ba, zan
masa waya ma na bashi hak'uri, bana son zuwa
guri ne na tarar da tarkacen mutane marasa aji
a gurin, wannan ne kawai badan wannan ba
zanje mana" "amma ai ka san waye Jabir! kuma
ka San waye mahaifinsa a garin nan, so bana
tunanin za'ayi k'aranta a gurin, ka sa ni ma ko
ka had'u da wata 'yar minister acan ya fad'a
yana murmushi.
Ya tsine fuska Abeed ya yi, yace" ' ya'yan
ministers ai suna suka tana, kamar 'yar k'
aramin minister mai zan yi da ita" shi dai
Mubarak ido kawai ya zuba yana kallonsa domin
al'amarin Abeed ya girmi tunaninsa, da k'yar ya
samu ya lalla6ashi ya amince akan zai je.
Muje zuwa muji mizai faru a gun.......
Www.hauwajabo.blogspot.com
Www.jabohauwa.WordPress.com
M Twins?? & Auntie M. Jabo ??
[4/11, 2:54 PM] Wacce Zamuyi Book: ??AN YI
WALK'IYA 9??
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Cikin 6acin rai Abeed ya koma gida, parking
kawai ya yi ko kulle motar bai yi ba, ya wuce
part d'in sa, ransa a dagule yake gaba d'aya,
yana tunanin wai yaushe ne burinsa zai ciki, ya
samu yarinyar da ta dace da shi, wacce ya ke
mafarkin samu, domin shi kansa yanzu ya
hak'ik'an ce da ya na buk'atar aure, amma
matsalar duk 'yan matan da ke sonsa yanzu ya
raina arzikin iyayensu, duk da cikin su babu
wadda za a d'auka ace babanta matsiyaci ne,
don dai shi ya d'auki k'atoton buri ya sakawa
zuciyarsa, dole sai 'yar mai hannu da shuni,
lokaci d'aya ya tuna da wacce akace tanasonsa,
wai babanta yayi rik'on logal government, dai
rainin wayo, wani dogon tsaki yaja, yadan juya
kwanciyar sa, ya kalli a gogon d'akin yana
lumshe ido.
*********
Goggo wacce nake tunanin y'ar uwar Dadyn su
Abeed ce, zaune take tareda Mumy suna hira,
Abeed ne ya shigo ya gaishesu cikin sakin fuska
sannan ya wuce d'akin sa, nan suka fara hirar
yau da kullum, har Goggo ta gangaro akan
abinda ya dad'e yana damun ta,
"hajiya yaran yanzu sai a hankali, sam basa
tunani basa naziri, yanzu za ku ga wasu yaran
masu kud'i idan za su yi aure sai su rik'a
hangen wadda mahaifin ta ya dame nasu ya
shanye da naira, don zilama, maimakon su nemi
dai_dai su, tunda Malam bahaushe ma ya ce
"dai_dai ruwa dai_dai tsaki, kuma kowace
k'warya da abokin burminta" sannan ma ina
laifin su yi k'asa_k'asa su nemi 'yar talaka
bawan Allah suma su samu su lasa, kinga ai an
taimaki juna an rufawa juna asiri ta wannan
hanyar, amma ba a yi saboda buri ya cikawa
masu irin wannan halin zuciya, kowa sai dai-dai
shi," Mumy tace "Wallhy zancen ki dutse
Goggon yara, nima abin yana damuna,
musamman idan naga halin yaronnan banajin
dad'i sam, amma kinsan kosu talakawan akwai
nasu sabida sai su k'wallafa dogon buri wa
yaran su, su mayar da yayan nasu kamar jari,
domin wasu sai ka ga sun zaune jiran mai d'an
maik'o_maik'o har yarinya ta tsofe a gida, ba
iyayenba ba ' ya'yan ba, kije gida ki rasa gane
uwa da yaran gida, akwai wani gida da mukaje
ta'aziya, a gidan naga mata 'yar kyakyawa,
wacce nake tunanin zata haifi yara biyu ko uku,
nake tambayar matar gidan, an mata amarya ne,
dan tare na gansu, sai take cemin ai 'yar kice
wance, wallhy saida na kai zaunedDan mamaki,
na tuna yarinyar sa'ar Muhammad ce fa! Amma
har yanzu tana gida," Goggo ta saka dariya, "
kin bani dariya, wai an miki amarya ne" itama
Mumy dariyar tayi suka ci gaba da hira" wannan
zamanin kowa kwad'ayi ya yi masa yawa, bayan
sun mata Allah ke yin komai, domin kowa an
riga an rubuta k'addararsa tun kafin ya zo
duniyannan, we just trace, sai ka ga budurwa ta
zauna jiran Mr right har ta tsofe tun tana samun
masu zuwa har lokacin ta ya wuce ya zamana
bata samu, ta tashi a tutar babu, k'arshe sai ta
auri wanda bataso, sabida da yawa masu
wannan burin, wallhy basa auren mazan da
zuciyar su takeso, saidai dan kud'i, su tashi ba
wan ba k'ani, ta yi haihuwar guzuma 'ya kwance
uwa kwance, ba mai d'an maik'o_maik'o ba mijin
kwatakwata" nan ma saida suka dara, Goggo
tace, " nifa kina magana kina saka engilishi,
kuma kinsan ba ganewa nakeyiba," sukayi dariya
gaba dayan su, Goggo tace, " Allah ya sa masu
wannan halin su gano su bari dan ba alkhairi
acikinsa" ameen Mumy ta amsa dashi,
Na kalli M Twins nace "nifa al'amarin Abeed
yana bani mamaki domin ya d'ebo da zafi, kace
sai 'yar wane ko wane," M. Twins tace " ?kedai
bari Aunty Jabo, Allah na d'auka irin wannan
abin matane kawai keda wannan hali, ashe har
maza ma sunayi, abin kunya, amma hausawa
sun ce "kowa ya d'ebo da zafi bakinsa"..........."
Www.hauwajabo.blogspot.com
Www.jabohauwa.WordPress.com
M Twins??& Auntie M. Jabo ?????
[4/11, 2:54 PM] Wacce Zamuyi Book: ??AN YI
WALK'IYA 8??
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
K'arasawa ta yi in da Mufeeda ke tsaye kamar
an dasata ta ce "mufy ya na ganki a tsaye,
bayan ya tafi dama nasan ba lallai ya amince da
buk'ata na ba".
Cikin yak'e Mufeeda ta ce "kar ma ki yi wannan
tunanin Fadeela, zai so ki da yardar Allah, yanzu
ma don bai ganki ba ne na tabbatar idan ya yi
ido hud'u dake ba abinda zai hana ya so ki".
A jiyar zuciya Fadeela ta yi, sannan ta ce "ta
yaya zan kuma had'uwa da shi bare har ya
ganni?? Kar ki manta, ko sunansa ban sa ni ba,
bare in da ya ke".
Murmushi Mufeeda ta yi, ta ce " idan akan
wannan ne ki kwantar da hankalinki kamar
tsumma a randa, idan kullum kike son ganin
Abeed za ki gan shi da yardar Allah."
Cikin mamaki Fadeela ta ce "wow! nice name,
sunansa kenan"?
Mufeeda ta gyad'a kai alamar eh, Fadeela ta
cigaba da fad'in "amma mufy ta yaya zan gan
shi duk lokacin da na ke so ya gaya miki sunan
unguwarsu ne, ko wurin aikinsa ?"
Dariya Mufeeda ta yi sosai sannan ta ce"
wannan kuma sai kin ba da wani abu sannan
zan gaya miki, "6ata rai Fadeela ta yi cikin sigar
wasa ta ce" dad'ina da ke kenan, yanzu za ki
fara ja mun rai tunda kin ga ina son ji ".
Tafiya Mufeeda ta fara tana cewa" shi kenan
tunda ba kya son ji, da tuni kin mik'o wani abu,
"gabanta Fadeela ta tara tare da cewa" haba
friendy ko haka ki ka bar ni ai kin ja mun rai,
don Allah ki gaya mun", ta k'arashe maganar
kamar za ta yi kuka.
Mufeeda ta ce "don't cry k'awata, he's my
cousin", waro ido Fadeela ta yi tare da daka
tsalle ta rungume Mufeeda tana cewa "don
Allah da gaske kike yi mufy"?
Mufeeda ta ce" yes da gaske ne ko gobe ki ke
so zan kaiki gidansu ya Abeed, "Fadeela ta
kuma k'ank'ameta tare da cewa amma na ji
dad'i Allah ya sa hakan ya zama silar cikar
burina." Mufeeda ta ce "ameen, sannan ta duba
agogon wayarta ta ce" gaskiya Fadeela dare
yayi fa, gashi lunching d'in an fara a makare bari
na kira driver ya zo, sai ya fara kai ki gida,
sannan sai mu wuce ".
Fadeela ta ce" gaskiya kam don kar ayi mana
fad'a kinsan hajiya idan ta fara," suka saka
dariya.
Www.hauwajabo.blogspot.com
Www.jabohauwa.WordPress.com
M Twins ?? & Auntie M. Jabo ?????
[4/11??AN YI WALK'IYA 6&7 ??
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Tun da safiyar ranar mubarak yake ma Abeed
waya akan kada ya manta please, yamai SMS ba
adadi, k'arshe ya yarda zai tafi, dan har ya
shirya dojewa.
Sai wurin k'arfe tara da minti ashirin da biyar
Abeed da tawagarsa suka shiga hall d'in, cikin
takun isa da k'asaita yake tafiya, ya rufe idonsa
da wani shade bak'i kaitsaye gurin da aka
tanada domin zaman su suka nufa.
Wohoho! Ku zo ku ga 'yan mata yanda suka
zuba masa na mujiya suna kallo, kai basu kad'ai
ba har mazan dake gurin kallonsa suke yi
tamkar sun ga wata sabuwar halitta, shi kuwa
gogan naku ko kallo ba su ishe shi ba, tafiyarsa
kawai yake cikin isa da izza har ya isa wurin
zaman su.
Tun shigowarsa wata yarinya mai amsa sunan
Fadeela, muka ga duk ta rud'e ta rikice, sai wani
dube_dube take kamar mai neman wani abu.
Sai can kuma muka ga ta nufi wani side na
musamman, domin an yi decorating gurin sosai
fiye da inda take zaune,
Da sauri ta k'arasa wurin har tana tuntu6e, tare
da rik'o hannun wata budurwa wadda ba zata
wuce sa'arta ba, sannnan ta ce "Mufy ta so don
Allah ki gan shi shine wanda na ke yawan yi
miki maganarsa" ido Mufeeda ta zuba mata na
d'an lokaci sannnan ta ce" wai ki na nufin guy
d'in da ba ki da aiki sai na maganarsa shine ya
zo nan gurin,"?
Fadeela ta ce "eh tare da langa6ar da kanta
gefe,"
Mufeeda ta yi farr da ido,sannnan ta ce "gaskiya
fady kin ban kunya, duk yanda kika h'adun nan,
kuma kike gwara kan samari son ranki amma ki
6ige da baran soyayya akan saurayin da ko
sunansa ba ki sa ni ba".
Dafa kafad'arta Fadeela ta yi tare da cewa
"friendy ba ki ga guy d'in ba ne that's why kike
wannan maganar, kin san first class guy, full
options to shi ne, ni tsoro ma nake kar ki gan
shi ki kasa controlling kan ki ki je ki shigar da
kan ki ba ni ba" ta k'arashe maganar tare da
sakin dariya!
Duka Mufeeda ta kai mata, ta goce sannnan ta
ce "an gaya miki akwai wanda ya isa ya ture
gwamnatin k'albina ne," Mufeeda ta cigaba da
fad'in "ni dai zo ki nuna mun in da ya ke, ga
ganshi, na cigaba da abinda na ke yi".
Fadeela ta ce "na ga dai sun nufi wurin da aka
tanada don manya_manya abokan ango" ta
fad'a tana d'an kalle-kalle
OK, "to ta yaya zan yi na gane shi??" Cewar
Mufeeda, nari mu je na nuna miki shi ko daga
nesa ne, d'an nesa da su Fadeela ta tsaya take
nunawa Mufeeda shi, ba tare da ko na kusa da
su sun gane abinda suke yi ba.
Tun da Mufeeda ta hangoshi take wasiwasin
wani abu a zuciyarta, sai da ta zo daf da shi
sannan ta tabbatar da abinda take zato. Sallama
ta yi sannan ta ce "sannu yaya Abeed" Jin an
kira shi da yaya, ya tilasta masa d'agowa da kan
sa domin ganin mai magana.
Fuskarsa ya d'an saki sannan ya ce " yawwa
sannunki", ta cigaba da fad'in ashe kai ma ka zo
bikin k'awarmu"?? Jin bai ce komai, ta ce
"angon ne abokinka ke nan"??
kai ya gyad'a mata kawai, ta ce" ai ni amaryar
ce close friend d'ina".
Jin ya kuma shiru ta ce "yaya ba ka son zuwa
gidanmu su Arfat ne kawai ke zuwa".
Hmm! kawai ya ce, nan ma shiru ne ya kuma
ratsawa, sai da ta ga shirun yayi yawa ta ce
"dama akwai maganar da ta kawoni wurinka
idan ba za ka damu ba ka ba ni 5 minute's
please", kamar ba zai yi magana ba, sai can ya
mik'e ya yi mata nuni da su fita daga gurin.
Gefe suka koma, sannan ta fara masa bayanin
abinda ya kawota, ta k'arashe maganarta da
cewa don Allah yaya ka taimakawa k'awata ba
ka ga yadda ta ke sonka ba."
Bud'ar bakinsa sai ya ce "waye mahaifinta"?
Cikin rashin fahimtar maganarsa Mufeeda da ta
ce" Babanta dai d'an siyasa ne", ya ce
"muk'amin meye da shi"?
eh, to ni dai abinda na sa ni ya ta6a rik'on
k'warya a local government".
"What!" ya fad'a da k'arfi, yana had'e fuska,
daga haka bai k'ara cewa da ita komai ba, sai
ga ni ta yi yana niyyar fita daga hall d'in ba ki
d'aya. Da sauri ita ma ta bi bayansa,bayan ya
isa in da ya ajiye motarsa yana k'ok'arin shiga,
ta sha gabansa tana fad'in "haba yaya Abeed ba
ka ce komai ba, ba ka ga yanda yarinyar take
mutuwar sonka ba".
Ai kuwa sai dai ta mutu in dai ni ne, I hate her,
ya fad'a tare da shigewa mota ya ja da k'arfi da
niyyar ficewa daga wurin, dai_dai lokacin
Fadeela ta fito..........................
Www.hauwajabo.blogspot.com
Www.jabohauwa.WordPress.com
M Twins ?? & Auntie M.Jabo ?????
[4/11, 2:54 PM] Wacce Zamuyi Book: ??AN YI
WALK'IYA 10&11 ??
©Mrs Saif & Hauwa M Jabo
®NWA
Bayan kwana uku Mufeeda da Fadeela suka yi
shirin zuwa gidansu Abeed don gaishe da Mumy,
sun taki sa a kuwa don sun tarar da Arfat da
afrat suna gida, su na yin sallama, Arfat ta taso
da sauri ta rungume Mufeeda tana fad'in
"oyoyo! Mufeeda yau a gidanmu" ?
Kafin ta yi magana, Mumy ta fito, nan da nan ita
da Fadeela suka zube su na gaisheta, cikin
fara'a Mummy ta amsa musu, sannan ta ce
"Mufeeda shiru kwana biyu kin daina lek'o mu".
Mufeeda ta ce "eh wallhy Mummy school ne ya
6oyeni", mummy ta ce " ayya!, nima nasan
Mufeeda akwai zumunci, to Allah ya ba da sa
a", suka ce ameen ".
Sai kuma ta kalli Fadeela ta ce da Mufeeda"
Wannan k'awarki ce "?
Murmushi Mufeeda ta yi tana kallon Fadeela ta
ce" eh,
Mummy k'awa ta ce " Allah sarki ya sunanta"?
Tace" Fadeela ", sannu Fadeela Mummy ta fad'a
tare da mik'ewa ta na cewa" Arfat haka za ku
bar bak'in naku ba d'an abun ta6awa "?
Afrat ta ce" Mummy dama yanzu na ke son
tashi", ya dai kamata Mummy ta fad'a tare da
shigewa kitchen.
Sun sha hira sosai, sannan daga bisani Mufeeda
take ce da Arfat ya Abeed na nan kuwa??
Arfat ta ce "a'a, ina za ki ga ya Abeed yanzu, ai
sai wurin k'arfe biyar yake dawowa daga
office". Mufeeda ta ce "ok, Arfat ta ce" ko ta
samu ne "ta fad'a tana murmushi, ita ma
Mufeeda murmushin ta yi, sannan ta ce "sosai
kuwa, Fadeela ce ke masifar son ya Abeed,"
Arfat ta ce "wow! ai kuwa ina ganin Fadeela na
ji ta kwanta mun a rai, Allah ya sa ya Abeed ya
amince, gaskiya da ya yi mata".
Sai kuma ta mik'e da sauri ta na fad'in bari na
je na sanarda Mummy ta zo ga sirikarta",
Fadeela ta hanzarinta ta rik'o hannun Arfat tana
Murmushi ta ce "don Allah kar ki gaya mata
yanzu bari sai mun tafi Allah kunya nake ji, ita
kanta Mufy ta san ba halina ba ne cewa ina son
wani kawai na d'auki son yayanki a wani
6angare na k'addarata, amma kwata_kwata
mace ta ce tana son namiji baya burgeni", ta
k'arashe maganarta da d'an guntun hawaye.
Dukan su jikinsu ya yi sanyi Arfat ta ce "in dai
mummy ce ba ta da matsala Allah ki daina ma
Jin kunya don ta saba ganin 'yan mata
kala_kala masu zuwa neman ya Abeed".
Har wurin k'arfe shida Abeed bai dawo ba, don
haka suka yi shirin komawa gida, mummy ta
had'a musu sha tara ta arziki, sannan ta saka
driver ya kai su gida.
Sai wurin k'arfe bakwai ya shigo gidan , bayan
ya yi wanka ya ci abinci, mummy ta same shi
tace ta na son yin magana da shi. Murmushin
gefen kumatu ya yi sannan ya ce "ina Jin ki
Mum".
Mummy ta fara magana "Abeed dama akan
maganar aurenka ne, gaskiya ya kamata ka
nutsu kasan mai kake yi zuwa yanzu, ka ajiye
duk wani shirme da ke ranka, ka za6i matar
aure ka yi aurenka ya fiye maka, kuma mu ma
zamu fi samun kwanciyar hankali, don na gaji da
zaryar da 'yan mata ke mana a cikin gidan nan".
Juyo da dubansa ya yi sosai gareta, sannan ya
ce "Mum yau ma wata ta zo kenan"?
Mummy ta ce "eh yarinya mai hankali da kunya
da za ka bi maganata da ka nemeta, don daga
gani ' yar gidan mutunci ce".
Yace "Mum ba ki gane ba ne ni fa duk 'yan
matan da ke zuwa gidan nan ba ni na ke cewa
su zo ba,in fact wasu ban ma ta6a ganinsu ba,
kuma har yanzu ban samu wadda na ke so ba,
please Mum adaina takura ni akan wad'ancan '
yan matan wahala ce bata ishe su ba that's all".
Da haka ya mik'e yana shirin tafiya Mummy ta
ce "yanzu Abeed za ka so ' yan uwanka su
Arfat su fad'a irin Wannan halin a fad'i irin
abinda ka fad'a a kansu, don nasan yadda ka ke
son su".
Ya ce "no Mummy nasan ba za su yi irin
wannan halin ba, Mummy ta ce" shi kenan dai,
idan Daddynku ya dawo za mu tattauna akan
maganar, je ka kawai"..............
Mum Twins ?? & Auntie M Jabo ??
M Twins??& Auntie M. Jabo ?????
??AN YI WALK'IYA 8??
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
K'arasawa ta yi in da Mufeeda ke tsaye kamar
an dasata ta ce "mufy ya na ganki a tsaye,
bayan ya tafi dama nasan ba lallai ya amince da
buk'ata na ba".
Cikin yak'e Mufeeda ta ce "kar ma ki yi wannan
tunanin Fadeela, zai so ki da yardar Allah, yanzu
ma don bai ganki ba ne na tabbatar idan ya yi
ido hud'u dake ba abinda zai hana ya so ki".
A jiyar zuciya Fadeela ta yi, sannan ta ce "ta
yaya zan kuma had'uwa da shi bare har ya
ganni?? Kar ki manta, ko sunansa ban sa ni ba,
bare in da ya ke".
Murmushi Mufeeda ta yi, ta ce " idan akan
wannan ne ki kwantar da hankalinki kamar
tsumma a randa, idan kullum kike son ganin
Abeed za ki gan shi da yardar Allah."
Cikin mamaki Fadeela ta ce "wow! nice name,
sunansa kenan"?
Mufeeda ta gyad'a kai alamar eh, Fadeela ta
cigaba da fad'in "amma mufy ta yaya zan gan
shi duk lokacin da na ke so ya gaya miki sunan
unguwarsu ne, ko wurin aikinsa ?"
Dariya Mufeeda ta yi sosai sannan ta ce"
wannan kuma sai kin ba da wani abu sannan
zan gaya miki, "6ata rai Fadeela ta yi cikin sigar
wasa ta ce" dad'ina da ke kenan, yanzu za ki
fara ja mun rai tunda kin ga ina son ji ".
Tafiya Mufeeda ta fara tana cewa" shi kenan
tunda ba kya son ji, da tuni kin mik'o wani abu,
"gabanta Fadeela ta tara tare da cewa" haba
friendy ko haka ki ka bar ni ai kin ja mun rai,
don Allah ki gaya mun", ta k'arashe maganar
kamar za ta yi kuka.
Mufeeda ta ce "don't cry k'awata, he's my
cousin", waro ido Fadeela ta yi tare da daka
tsalle ta rungume Mufeeda tana cewa "don
Allah da gaske kike yi mufy"?
Mufeeda ta ce" yes da gaske ne ko gobe ki ke
so zan kaiki gidansu ya Abeed, "Fadeela ta
kuma k'ank'ameta tare da cewa amma na ji
dad'i Allah ya sa hakan ya zama silar cikar
burina." Mufeeda ta ce "ameen, sannan ta duba
agogon wayarta ta ce" gaskiya Fadeela dare
yayi fa, gashi lunching d'in an fara a makare bari
na kira driver ya zo, sai ya fara kai ki gida,
sannan sai mu wuce ".
Fadeela ta ce" gaskiya kam don kar ayi mana
fad'a kinsan hajiya idan ta fara," suka saka
dariya.
Www.hauwajabo.blogspot.com
Www.jabohauwa.WordPress.com
[4/11, 2:54 PM] : ??AN YI WALK'IYA 12&13
??
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Ana kiraye_kirayen sallar isha'i Daddy ya dawo,
kaitsaye masallacin manne da gidan ya nufa
domin sauke farali, bayan an idar da sallah tare
suka fito da Abeed zuwa cikin gidan, suna tafe
suna hirarsu irin ta d'a da uba, Mummy suka
tarar a parlor ta na jiran k'arasowar mai gidan
nata, cikin fara'a da girmamawa ta yi masa
sannu da zuwa, tana fad'in "dama na ce yanzu
haka masallaci ka wuce", Daddy ya ce "eh na
shigo ana shirin ta da sallah na ce bari na yi
sallar in yaso kawai na shigo gaba d'aya" ya
fad'a yana murmushi
Mummy ta ce "gaskiya kam, yanzu dai ga abinci
nan an kammala kai kawai mu ke jira", ok, bari
na je na watsa ruwa takun, Daddy ya fad'a ya
na shirin barin wurin.
Sai wurin 8:30 suka zauna cin abincin, bayan
sun kammala ne kowa ya yi hani'an, don su
Abeed har sun bar wurin, Mummy ke sanar da
Daddy maganar Abeed, ta k'arashe maganar da
cewa "gaskiya Alhaji ya kamata a d'auki mataki
akan maganar Abeed, don yanzu kusan
sa'anninsa duk sun yi aure, wasu har sun fara
tara yara, amma shi shiru ko zancen auren ba
ya yi, ni abinda ma ya fi damuna shine k'udirin
da ya d'auka ya saka a zuciyarsa na lallai shi
sai 'yar gidan hamshak'in mai kud'i zai aura,
bayan da talaka da mai kud'i duk na Allah ne".
Gyd'a kai Daddy ya yi, ya ce "haka ne, amma kin
san abinda za a yi"?
Mummy ta ce " a'a, ya ce "dama Alhaji Usman
tun kwanakin baya yake maganar mu had'a
Abeed aure da 'yar wajensa Hafat, na ce da shi
sai na yi shawara da ke, da kuma shi Abeed
d'in, don bana son na takura shi akan abinda
baya so, shi yasa na ba shi dama duk tsawon
wannan shekarun, amma tunda abun na shi haka
ya zama, lallai_lallai ki gaya masa ya je ya ga
yarinyar su daidaita kansu, tunda ai yasan gidan,
don Alhaji Usman ba 6oyayyene ba a wurinsa."
Mummy ta ce "Allah dai ya sa ya amince, don
lamarin na Abeed sai addu'a", Daddy ya ce "da
kakkausar murya za ki gaya masa ni na ce ya je,
idan dai ban da k'uruciya yaran gidan Alhaji
Usman mai za a nuna musu, suna da tarbiya ga
hankali ga ilimi, amma shi ya tsaya neman
k'yale_k'yalen duniya da ba zai anfaneshi da
komai ba sai wahala".
Mummy ta ce " wallahi kam, ai yaran yanzu
ba sa gane abinda ake hango musu, sai abinda
zuciyarsu ta raya musu shi suke yi, bayan
bahaushe yace " son zuciya 6acinta".
Daddy ya ce "sosai Allah dai yasa mu ga
ne", mummy ta bi shi da ameen".
*********
Tun da safe Abeed ya yi shirin zuwa office
kamar yadda ya saba, duk safiya kafin ya wuce
office sai ya je ya yiwa mummy sallama ita da
Daddy in dai ya na gari ko bai yi sammakon fita
ba.
Bayan ya shiga mummy ke sanar da shi
yanda suka yi da Ddynsa akan maganar neman
auren 'yar gidan Alhaji Usman, zaro ido waje ya
yi yana fad'in "Mum wai wani Alhaji Usman"?
Mummy ta ce" akwai wani Alhaji Usman bayan
aminin Daddyn ku"?
Mere baki gefe ya yi, sannan ya ce "Mum mun
San fa komai gameda Alhaji Usman kawai dai
muna shiru ne."
Fito da ido waje ta yi, ta ce" mai ka sa ni game
da shi? yana da wani mugun Hali ne"?
Abeed ya ce "no ba abinda na ke nufi ba kenan,
kawai dai a takaice yaron Daddy ne, don dai
Daddy ya taimaka masa ya ba shi companyn sa
da ke bompai ne ya na kula da shi, shi ne kawai
ake ganinsa wani mai arzik'i, kin ga kuwa Mum
kamar ni haka, ta yaya zan auri 'yar yaron
babana!!! Ai na ci baya sosai, gaskiya mum
bazan ma iya ba."
Mummy da tunda ya fara magana take tafa
hannu tana sallati tace "yanzu Abeed tanan ka
6ullo kuma"?
Ya ce " Mummy don dai kin san Daddy da rik'on
abokanai ne na tun k'uruciya amma ba don haka
ba, ina laifin ko a cikin manya_manya attajiran
garin nan ya nema mun 'yar wani perhaps da na
amince na yi manage da ita."
Mummy kam tuni ta dask'are a gurin don
mamaki, tace "au maneji ma za ka yi da ita"? To
bari Alhaji ya dawo na gaya masa, gaskiya ya
nemo mai ruk'iyya ya duba ka don ina ga ba
zaka rasa jinnu ba".
Dariya sosai Abeed ya yi sannan ya ce
"Mum wallahi ras na ke, kawai dai na gaya miki
abinda ke zuciya ta ne," sai kuma ya kalle
agogon dake daure a hannunsa ya Ce "Mum
gaskiya na makara bari na tafi sai na dawo,"
Mummy tace "Allah ya kiyaye hanya", yace
"ameen tare da ficewa daga
d'akin......................
Mum Twins ?? & Auntie M Jabo ??
[4/11??AN YI WALK'IYA 9??
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Cikin 6acin rai Abeed ya koma gida, parking
kawai ya yi ko kulle motar bai yi ba, ya wuce
part d'in sa, ransa a dagule yake gaba d'aya,
yana tunanin wai yaushe ne burinsa zai ciki, ya
samu yarinyar da ta dace da shi, wacce ya ke
mafarkin samu, domin shi kansa yanzu ya
hak'ik'an ce da ya na buk'atar aure, amma
matsalar duk 'yan matan da ke sonsa yanzu ya
raina arzikin iyayensu, duk da cikin su babu
wadda za a d'auka ace babanta matsiyaci ne,
don dai shi ya d'auki k'atoton buri ya sakawa
zuciyarsa, dole sai 'yar mai hannu da shuni,
lokaci d'aya ya tuna da wacce akace tanasonsa,
wai babanta yayi rik'on logal government, dai
rainin wayo, wani dogon tsaki yaja, yadan juya
kwanciyar sa, ya kalli a gogon d'akin yana
lumshe ido.
*********
Goggo wacce nake tunanin y'ar uwar Dadyn su
Abeed ce, zaune take tareda Mumy suna hira,
Abeed ne ya shigo ya gaishesu cikin sakin fuska
sannan ya wuce d'akin sa, nan suka fara hirar
yau da kullum, har Goggo ta gangaro akan
abinda ya dad'e yana damun ta,
"hajiya yaran yanzu sai a hankali, sam basa
tunani basa naziri, yanzu za ku ga wasu yaran
masu kud'i idan za su yi aure sai su rik'a
hangen wadda mahaifin ta ya dame nasu ya
shanye da naira, don zilama, maimakon su nemi
dai_dai su, tunda Malam bahaushe ma ya ce
"dai_dai ruwa dai_dai tsaki, kuma kowace
k'warya da abokin burminta" sannan ma ina
laifin su yi k'asa_k'asa su nemi 'yar talaka
bawan Allah suma su samu su lasa, kinga ai an
taimaki juna an rufawa juna asiri ta wannan
hanyar, amma ba a yi saboda buri ya cikawa
masu irin wannan halin zuciya, kowa sai dai-dai
shi," Mumy tace "Wallhy zancen ki dutse
Goggon yara, nima abin yana damuna,
musamman idan naga halin yaronnan banajin
dad'i sam, amma kinsan kosu talakawan akwai
nasu sabida sai su k'wallafa dogon buri wa
yaran su, su mayar da yayan nasu kamar jari,
domin wasu sai ka ga sun zaune jiran mai d'an
maik'o_maik'o har yarinya ta tsofe a gida, ba
iyayenba ba ' ya'yan ba, kije gida ki rasa gane
uwa da yaran gida, akwai wani gida da mukaje
ta'aziya, a gidan naga mata 'yar kyakyawa,
wacce nake tunanin zata haifi yara biyu ko uku,
nake tambayar matar gidan, an mata amarya ne,
dan tare na gansu, sai take cemin ai 'yar kice
wance, wallhy saida na kai zaunedDan mamaki,
na tuna yarinyar sa'ar Muhammad ce fa! Amma
har yanzu tana gida," Goggo ta saka dariya, "
kin bani dariya, wai an miki amarya ne" itama
Mumy dariyar tayi suka ci gaba da hira" wannan
zamanin kowa kwad'ayi ya yi masa yawa, bayan
sun mata Allah ke yin komai, domin kowa an
riga an rubuta k'addararsa tun kafin ya zo
duniyannan, we just trace, sai ka ga budurwa ta
zauna jiran Mr right har ta tsofe tun tana samun
masu zuwa har lokacin ta ya wuce ya zamana
bata samu, ta tashi a tutar babu, k'arshe sai ta
auri wanda bataso, sabida da yawa masu
wannan burin, wallhy basa auren mazan da
zuciyar su takeso, saidai dan kud'i, su tashi ba
wan ba k'ani, ta yi haihuwar guzuma 'ya kwance
uwa kwance, ba mai d'an maik'o_maik'o ba mijin
kwatakwata" nan ma saida suka dara, Goggo
tace, " nifa kina magana kina saka engilishi,
kuma kinsan ba ganewa nakeyiba," sukayi dariya
gaba dayan su, Goggo tace, " Allah ya sa masu
wannan halin su gano su bari dan ba alkhairi
acikinsa" ameen Mumy ta amsa dashi,
Na kalli M Twins nace "nifa al'amarin Abeed
yana bani mamaki domin ya d'ebo da zafi, kace
sai 'yar wane ko wane," M. Twins tace " ?kedai
bari Aunty Jabo, Allah na d'auka irin wannan
abin matane kawai keda wannan hali, ashe har
maza ma sunayi, abin kunya, amma hausawa
sun ce "kowa ya d'ebo da zafi bakinsa"..........."
Www.hauwajabo.blogspot.com
Www.jabohauwa.WordPress.com
M Twins ?? & Auntie M. Jabo ?????
[4/11, 2:54 PM]??AN YI WALK'IYA 14&15 ??
©Mrs Saif & Hauwa M Jabo
®NWA
Daddy na dawowa Mummy ta kwashe yanda
suka yi da Abeed ta fad'a masa, ai kuwa ya yi
ta fad'a, nan take ya d'auki waya yace "da
Abeed duk abinda ya ke yi ya ajiye ya zo yana
kiransa", Abeed ya ce "to Daddy ga ni nan
zuwa" don dama ya san sai an yi haka, cikin
abinda bai fi 10 minutes ba ya shigo gidan,
kaitsaye parlourn Daddy ya nufa, bayan ya
gaishe su, Daddy ya fara magana "Abeed ka
saurare ni ka ji abinda zan gaya Maka, domin
maryam ta gaya mun duk yanda ku ka yi da ita,
to bari ka ji bazan d'auki wannan shashancin ba,
dole ka bi maganata idan ba haka ba, ka sanni
sarai".
Rausayar da kai Abeed ya yi ya ce "Daddy
dama abinda ya............" dakatar da shi Daddy
ya yi ta hanyar d'aga masa hannu, yace "ba na
son jin wata magana yanzu kawai tashi ka je ka
yi abinda na saka ka".
Jiki a sanyaye Abeed ya tashi yana fad'in "to".
Daga nan dakinsa ya wuce, amma zuciyarsa a
cunkushe take yana tunanin meye mafita, don
dai shi ya hak'ik'ancewa zuciyarsa ba zai ta6a
auren 'yar gidan Alhaji usman ba, ya san
kwata_kwata ba ajinsa ba ce, da wannan
sak'e_sak'en har barci ya yi awon gaba da shi.
Ko da ya tashi da safe fuskar nan tasa ba
annuri, su Arfat ma da suka ga yanayinsa tuni
suka kama kan su, tare da gimtse dariyar da ke
cin su, domin mummy ta gaya musu duk abinda
ake ciki, bayan ya fita ne Arfat ta kalli Afrat ta
ce "ni wallahi gwanda da Daddy ya yi wa ya
Abeed haka ko ya maida hankali ya yi auren, mu
ma mu fara ganin babies a gidanmu".
Afrat ta ce "ni kuma gani na yi da Daddy ya
kyale shi ya za6a da kan sa, idan ya ga bai
samu wadda ya ke so ba ai dole ya yi hak'uri ya
auri wata,kuma ni yaran gidan Alhaji Usman ba
su yi mun ba, sai gwalli da iyayi amma ba su da
wani kyau".
Murmushi Arfat ta yi sannan ta ce "Ai k'arshen
mai ruwan ido ke nan".
Bayan ya dawo daga aiki mummy ta takurashi
akan ya je su gana da Hafsat, dole ba yanda ya
iya ya yi shirin zuwa gidan Alhaji Usman.
Duk da ya saba shiga har cikin gidan a duk
lokacin da ya je, amma wannan zuwan da ya yi
tsayawa ya yi a inda ya yi parking motarsa, sai
da mai gadin gidan ya ga ba shi da niyyar shiga
ciki don ya ga ya dade a tsaye sannan ya je ya
ce da shi, "yalla6ai Alhajin ya na ciki ka k'arasa
mana", juyawa ya yi ya kalleshi ya ce "ai ba
wurinsa na zo ba, ka je ka ce ana kiran Hafsat"
Mai gadi ya ce "to bari na je na gaya mata" bai
fi minti biyu da tafiya ba, ya dawo ya ce "ta ce
tana zuwa".
Hafsat kuwa tunda mai gadi ya sanarda ita ana
sallama da ita, ta tambaye shi waye ya ce da
ita Abeed ne, ta shiga tsallen murna, dama ba
ta dad'e da fitowa daga wanka ba, nan da nan
ta hau kwalliya a fenta can a manna can har ta
gama, ta fito cas da ita.
Dama mai gadi ya gaya mata yana bakin gate so
direct can ta nufa, ana tafe ana yauk'i, kamar
ba za a taka ba, sai kuma jikinta ya yi sanyi
lokacin da ta fara hangoshi, don yanayinsa ya fi
kama da wanda aka aikowa sak'on mutuwa, sai
ta fara tunanin ko wani mugun sako ya kawo
mata ne! Daurewa ta yi ta k'arasa inda ya ke
ta masa sallama tare da fad'in "sannu da zuwa",
sallamar kawai ya amsa ya yi shiru, sun yi
kusan 4 minutes ba wanda ya k'ara cewa komai,
sai can Hafsat ta ce "ai da ka zo mun k'arasa
ciki ko"?
A'a kawai ya ce da ita, ta ce" ai tsayuwar ce ba
dad'i, ko za ka zo mu koma daga can wurin ta
yi nuni da wani wuri d'an nesa da su kad'an da
aka sawa rumfa tare da resting chairs, ya ce
"ba zama zan yi ba, don yanzu haka bai fi 5
minutes na tafi ba", Hafsat a ranta ta ce anya
kuwa Abeed ya na sonta? wata zuciyar ta ba ta
amsa da cewa ai da yana sonki da tunda kika zo
kin gani a fuskarsa, kawai dai........... Abeed ne
ya katse mata tunani ta hanyar yin magana,
yace "ba sai na miki dogon bayani, don na San a
gida an miki bayanin komai, duk da dai ke ban
san tunaninki akaina ba, amma ni zan gaya miki
gaskiyar abinda ke zuciya ta, ni ban yarda da
wannan auren had'in ba, kuma ba zan iya
bijirewa maganarsu ba, kuma ke kin san duk
burin mace bai wuce ta samu miji mai sonta da
kaunarta ba sannan yake kuma tausayinta ba,
don shi ne a kowane irin hali zai kasance tare
da ita, idan dai ki na buk'atar hakan to kada ki
kuskura ki amince da aurena, shawara ce na ke
ba ki idan ki d'auka kin taimaki kan ki, idan
kuma ba haka ba a shirye na ke da d'aukan duk
wani k'alubale sannan zan aureki, smma zaki
rasa duk wayanchan abubuwan idan kin shirya
bismillah!!".
Bai jira abinda za ta ce ba, ya fad'a mota ya
yi mata key ya fice daga gidan.
Hafsat kuwa ta fi k'arfin 10 minutes a tsaye a
wurin tana maimaita kalamansa, sai da ta ga
hakan ba mafita ba ne ta shuri k'afafuwanta ta
shige ciki.............
Mum Twins ?? & Auntie M Jabo ??
[4/11, 2:54 PM] ??AN YI WALK'IYA 6&7 ??
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Tun da safiyar ranar mubarak yake ma Abeed
waya akan kada ya manta please, yamai SMS ba
adadi, k'arshe ya yarda zai tafi, dan har ya
shirya dojewa.
Sai wurin k'arfe tara da minti ashirin da biyar
Abeed da tawagarsa suka shiga hall d'in, cikin
takun isa da k'asaita yake tafiya, ya rufe idonsa
da wani shade bak'i kaitsaye gurin da aka
tanada domin zaman su suka nufa.
Wohoho! Ku zo ku ga 'yan mata yanda suka
zuba masa na mujiya suna kallo, kai basu kad'ai
ba har mazan dake gurin kallonsa suke yi
tamkar sun ga wata sabuwar halitta, shi kuwa
gogan naku ko kallo ba su ishe shi ba, tafiyarsa
kawai yake cikin isa da izza har ya isa wurin
zaman su.
Tun shigowarsa wata yarinya mai amsa sunan
Fadeela, muka ga duk ta rud'e ta rikice, sai wani
dube_dube take kamar mai neman wani abu.
Sai can kuma muka ga ta nufi wani side na
musamman, domin an yi decorating gurin sosai
fiye da inda take zaune,
Da sauri ta k'arasa wurin har tana tuntu6e, tare
da rik'o hannun wata budurwa wadda ba zata
wuce sa'arta ba, sannnan ta ce "Mufy ta so don
Allah ki gan shi shine wanda na ke yawan yi
miki maganarsa" ido Mufeeda ta zuba mata na
d'an lokaci sannnan ta ce" wai ki na nufin guy
d'in da ba ki da aiki sai na maganarsa shine ya
zo nan gurin,"?
Fadeela ta ce "eh tare da langa6ar da kanta
gefe,"
Mufeeda ta yi farr da ido,sannnan ta ce "gaskiya
fady kin ban kunya, duk yanda kika h'adun nan,
kuma kike gwara kan samari son ranki amma ki
6ige da baran soyayya akan saurayin da ko
sunansa ba ki sa ni ba".
Dafa kafad'arta Fadeela ta yi tare da cewa
"friendy ba ki ga guy d'in ba ne that's why kike
wannan maganar, kin san first class guy, full
options to shi ne, ni tsoro ma nake kar ki gan
shi ki kasa controlling kan ki ki je ki shigar da
kan ki ba ni ba" ta k'arashe maganar tare da
sakin dariya!
Duka Mufeeda ta kai mata, ta goce sannnan ta
ce "an gaya miki akwai wanda ya isa ya ture
gwamnatin k'albina ne," Mufeeda ta cigaba da
fad'in "ni dai zo ki nuna mun in da ya ke, ga
ganshi, na cigaba da abinda na ke yi".
Fadeela ta ce "na ga dai sun nufi wurin da aka
tanada don manya_manya abokan ango" ta
fad'a tana d'an kalle-kalle
OK, "to ta yaya zan yi na gane shi??" Cewar
Mufeeda, nari mu je na nuna miki shi ko daga
nesa ne, d'an nesa da su Fadeela ta tsaya take
nunawa Mufeeda shi, ba tare da ko na kusa da
su sun gane abinda suke yi ba.
Tun da Mufeeda ta hangoshi take wasiwasin
wani abu a zuciyarta, sai da ta zo daf da shi
sannan ta tabbatar da abinda take zato. Sallama
ta yi sannan ta ce "sannu yaya Abeed" Jin an
kira shi da yaya, ya tilasta masa d'agowa da kan
sa domin ganin mai magana.
Fuskarsa ya d'an saki sannan ya ce " yawwa
sannunki", ta cigaba da fad'in ashe kai ma ka zo
bikin k'awarmu"?? Jin bai ce komai, ta ce
"angon ne abokinka ke nan"??
kai ya gyad'a mata kawai, ta ce" ai ni amaryar
ce close friend d'ina".
Jin ya kuma shiru ta ce "yaya ba ka son zuwa
gidanmu su Arfat ne kawai ke zuwa".
Hmm! kawai ya ce, nan ma shiru ne ya kuma
ratsawa, sai da ta ga shirun yayi yawa ta ce
"dama akwai maganar da ta kawoni wurinka
idan ba za ka damu ba ka ba ni 5 minute's
please", kamar ba zai yi magana ba, sai can ya
mik'e ya yi mata nuni da su fita daga gurin.
Gefe suka koma, sannan ta fara masa bayanin
abinda ya kawota, ta k'arashe maganarta da
cewa don Allah yaya ka taimakawa k'awata ba
ka ga yadda ta ke sonka ba."
Bud'ar bakinsa sai ya ce "waye mahaifinta"?
Cikin rashin fahimtar maganarsa Mufeeda da ta
ce" Babanta dai d'an siyasa ne", ya ce
"muk'amin meye da shi"?
eh, to ni dai abinda na sa ni ya ta6a rik'on
k'warya a local government".
"What!" ya fad'a da k'arfi, yana had'e fuska,
daga haka bai k'ara cewa da ita komai ba, sai
ga ni ta yi yana niyyar fita daga hall d'in ba ki
d'aya. Da sauri ita ma ta bi bayansa,bayan ya
isa in da ya ajiye motarsa yana k'ok'arin shiga,
ta sha gabansa tana fad'in "haba yaya Abeed ba
ka ce komai ba, ba ka ga yanda yarinyar take
mutuwar sonka ba".
Ai kuwa sai dai ta mutu in dai ni ne, I hate her,
ya fad'a tare da shigewa mota ya ja da k'arfi da
niyyar ficewa daga wurin, dai_dai lokacin
Fadeela ta fito..........................
Www.hauwajabo.blogspot.com
Www.jabohauwa.WordPress.com

           By
HAYATU BABA ZUBAIRU
        (admin
   Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
          And
Cool novel, makeup and cooking)

      WHATSAPP NO:
       07039625239

M Twins ?? & Auntie M.Jabo ?????
[4/11, 2:54 PM] ??AN YI WALK'IYA 10&11
??
©Mrs Saif & Hauwa M Jabo
®NWA
Bayan kwana uku Mufeeda da Fadeela suka yi
shirin zuwa gidansu Abeed don gaishe da Mumy,
sun taki sa a kuwa don sun tarar da Arfat da
afrat suna gida, su na yin sallama, Arfat ta taso
da sauri ta rungume Mufeeda tana fad'in
"oyoyo! Mufeeda yau a gidanmu" ?
Kafin ta yi magana, Mumy ta fito, nan da nan ita
da Fadeela suka zube su na gaisheta, cikin
fara'a Mummy ta amsa musu, sannan ta ce
"Mufeeda shiru kwana biyu kin daina lek'o mu".
Mufeeda ta ce "eh wallhy Mummy school ne ya
6oyeni", mummy ta ce " ayya!, nima nasan
Mufeeda akwai zumunci, to Allah ya ba da sa
a", suka ce ameen ".
Sai kuma ta kalli Fadeela ta ce da Mufeeda"
Wannan k'awarki ce "?
Murmushi Mufeeda ta yi tana kallon Fadeela ta
ce" eh,
Mummy k'awa ta ce " Allah sarki ya sunanta"?
Tace" Fadeela ", sannu Fadeela Mummy ta fad'a
tare da mik'ewa ta na cewa" Arfat haka za ku
bar bak'in naku ba d'an abun ta6awa "?
Afrat ta ce" Mummy dama yanzu na ke son
tashi", ya dai kamata Mummy ta fad'a tare da
shigewa kitchen.
Sun sha hira sosai, sannan daga bisani Mufeeda
take ce da Arfat ya Abeed na nan kuwa??
Arfat ta ce "a'a, ina za ki ga ya Abeed yanzu, ai
sai wurin k'arfe biyar yake dawowa daga
office". Mufeeda ta ce "ok, Arfat ta ce" ko ta
samu ne "ta fad'a tana murmushi, ita ma
Mufeeda murmushin ta yi, sannan ta ce "sosai
kuwa, Fadeela ce ke masifar son ya Abeed,"
Arfat ta ce "wow! ai kuwa ina ganin Fadeela na
ji ta kwanta mun a rai, Allah ya sa ya Abeed ya
amince, gaskiya da ya yi mata".
Sai kuma ta mik'e da sauri ta na fad'in bari na
je na sanarda Mummy ta zo ga sirikarta",
Fadeela ta hanzarinta ta rik'o hannun Arfat tana
Murmushi ta ce "don Allah kar ki gaya mata
yanzu bari sai mun tafi Allah kunya nake ji, ita
kanta Mufy ta san ba halina ba ne cewa ina son
wani kawai na d'auki son yayanki a wani
6angare na k'addarata, amma kwata_kwata
mace ta ce tana son namiji baya burgeni", ta
k'arashe maganarta da d'an guntun hawaye.
Dukan su jikinsu ya yi sanyi Arfat ta ce "in dai
mummy ce ba ta da matsala Allah ki daina ma
Jin kunya don ta saba ganin 'yan mata
kala_kala masu zuwa neman ya Abeed".
Har wurin k'arfe shida Abeed bai dawo ba, don
haka suka yi shirin komawa gida, mummy ta
had'a musu sha tara ta arziki, sannan ta saka
driver ya kai su gida.
Sai wurin k'arfe bakwai ya shigo gidan , bayan
ya yi wanka ya ci abinci, mummy ta same shi
tace ta na son yin magana da shi. Murmushin
gefen kumatu ya yi sannan ya ce "ina Jin ki
Mum".
Mummy ta fara magana "Abeed dama akan
maganar aurenka ne, gaskiya ya kamata ka
nutsu kasan mai kake yi zuwa yanzu, ka ajiye
duk wani shirme da ke ranka, ka za6i matar
aure ka yi aurenka ya fiye maka, kuma mu ma
zamu fi samun kwanciyar hankali, don na gaji da
zaryar da 'yan mata ke mana a cikin gidan nan".
Juyo da dubansa ya yi sosai gareta, sannan ya
ce "Mum yau ma wata ta zo kenan"?
Mummy ta ce "eh yarinya mai hankali da kunya
da za ka bi maganata da ka nemeta, don daga
gani ' yar gidan mutunci ce".
Yace "Mum ba ki gane ba ne ni fa duk 'yan
matan da ke zuwa gidan nan ba ni na ke cewa
su zo ba,in fact wasu ban ma ta6a ganinsu ba,
kuma har yanzu ban samu wadda na ke so ba,
please Mum adaina takura ni akan wad'ancan '
yan matan wahala ce bata ishe su ba that's all".
Da haka ya mik'e yana shirin tafiya Mummy ta
ce "yanzu Abeed za ka so ' yan uwanka su
Arfat su fad'a irin Wannan halin a fad'i irin
abinda ka fad'a a kansu, don nasan yadda ka ke
son su".
Ya ce "no Mummy nasan ba za su yi irin
wannan halin ba, Mummy ta ce" shi kenan dai,
idan Daddynku ya dawo za mu tattauna akan
maganar, je ka kawai"..............
Mum Twins ?? & Auntie M Jabo ??
[4/11, 2:54 PM] ??AN YI WALK'IYA 21&22??
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Haka kuwa aka yi, don bayan teema Daddy ya
nemawa Abeed auren 'yan mata sun kai uku,
duka' ya' yan abokan sa ne , amma yanda ta
kasance da sauran suma haka takasance da su,
don duk a cikinsu bai katarin samun yarinyar da
ya ke mafarkin aura ba, don haka bai yi k'asa a
guiwa ba, wajen neman mafita ba, d'aya bayan
d'aya sai da ya nemi hanyar rabuwa dasu.
Daddy kuwa ransa ya kai k'ololuwar 6aci, don
Abeed ya kunya ta shi a idon abokan sa, kuma
ya watsa masa k'asa a ido, yanzu haka yana
cikin fushi da shi, kuma har yanzu yana nan
akan bakansa, na sai an yi auren kafin lokacin
da ya ce ya cika.
Yau kamar had'in baki, Mrs Saif dani M Jabo
duk mun makara zuwa gidansu Abeed don
d'auko muku rahoto, sai after 10pm muka isa
gidan, kaitsaye babban parlourn gidan muka
nufa, sai dai wayam ba kowa a ciki, said k'arar
A.C da kuma T V da ke ta 6a6atu ita kadai, ni
kam d'aya daga cikin kujerun dake parlourn na
samu na zauna, na juyo da dubana in da Jabo
ke tsaye, na ce
"Anya Auntie jabo yau za mu samu wani labari
kuwa"?
Jabo ta ce
"ni ma abinda na ke tunani ke nan maman
Twins, kalli fa hatta 'yan aikin dake saraftu ko
yaushe ba kowa duk sun shige, ko motsin su ba
a ji."
Na ce
"ko dai d'aki za mu bi su ne kawai"? Jabo ta
ce
"haka ma za mu yi, maybe baza mu rasa wani
abu acan ba, nan da nan kuwa na mik'e, muka
nufi d'akin Abeed, ko da muka shiga mun tarar
ya baje a lafiyayyen gadonsa sai sharar barci sa
yake yi, adole muka fito daga d'akin, tunda babu
abun rubutu a nan, d'akin su Arfat muka nufa
daga nan, sai dai suma duk maganar d'aya ce,
don kuwa suma sharar barcinsu suke yi hankali
kwance, bayan mun fito daga d'akin su afrat,
Jabo ke cewa "ni kuwa Mrs Saif lafiya mutanen
gidan nan yau suka yi barci da wuri haka"?
Na ce
"hmm! Ke ma ke fad'a kin riga ni fad'a ne
kawai, amma nima tunanin da na ke yi ke nan,
amma bari mu koma part d'in Mummy mu gani
ko akwai wani abun d'aukowa a can".
Side d'in mummy muka nufa gadan_gadan,
parlor muka fara shiga, ba kowa, daga nan muka
sulale muka fad'a bedroom d'in ta, nan ma shiru
ba kowa, sai muka yi zaton ko tana toilet ne,
muka d'an saurara amma ba mu ji alamar
mutum a ciki ba , almost 10mnts muna tsaye
muna jiran fitowar Mummy ammma shiru, har
sai da muka tabbatar wa kanmu cewa Mummy
bata part d'in ta kwata_kwata.
Ni kam Mrs Saif har na fara tsorata, na juya na
cewa
"Jabo gaskiya gidan nan ba lafiya ba".
Auntie jabo tace
"Nima abun ya d'aure mun kai, amma idan ba
lafiya ba, ta yaya su Abeed za suna sharar barci
irin haka"?
Na ce
"Da haka kuma, nima ga shi har na fara Jin
barci,gaskiya mu je kawai gobe ma dawo, M
Jabo tace "ni kaina barcin na ke ji".
Har mun fito, da niyyar tafiya sai muka ji kamar
sautin kukan Mummy yana tashi daga part d'in
Daddy, kasancewar ba nisa tsakaninsu, inkiya
Jabo ta yi mun akan na k'araso na ji kunsan
Jabo ba Dama wajen jin kwakwaf, sai da na
matsa daf da windown da ke d'akin na tabbatar
da Mummy ce ke shar6ar kuka, kallon_kallo
muka tsaya yi, muna tunanin mai ya saka
Mummy kuka irin haka, a cikin Daren nan,
maganar Daddy ce ta katse mana tunani, don
son Jin abinda ya ke fad'a ba mu San lokacin
da muka fad'a parlourn ba, Allah ya so suna
cikin d'aki, da asirin mu ya tonu.
Abinda muka ji Daddy na fad'a ne, ya tilasta
mana saka hannayen mu akan bakunan mu,
kada mu yi baran 6aramar fitar da sauti har su
an kara da mu a wajen.
Mummy muka jiyo tana yiwa Daddy magiya akan
ya hak'ura da maganar, koda Abeed zai tabbata
bai yi aure ba, Daddy ne ya fara magana a
hassle ya ce
"kin ga maryam, maganar nan dole a fade ta,
don komai lokaci ne, kuma ita magana lokacin
fita ne da ita, idan lokacin fitar ta ya yi, dole ta
fita."
Mummy muka hango ta yi baya ta zauna sharaf,
mu ma muna ganin haka, muka tattara inamu
inamu muka yi waje. Bayan mun fito ne muke
tattauna girman maganar da muka ji su Daddy
na yi, Auntie jabo ce ta ce
"gaskiya Mum Twins maganar nan ta d'aure
mun kai,"
na ce
"Ai ba ke kadai ba, nifa da ba tare muke ba da
sai nace ba daidai naji ba, ni kai na burina bai
wuce Allah ya kai mu gobe ba, mu zo mu ji
yanda maganar take dalla_dalla ba,"
M Jabo ta ce
"Ai ni ji na ke yi kamar yau na kwana a gidan
nan, don kar mu makara zuwa,"
na ce
"Ai kam dai.
Kuma readers sai ku biyo mu don Jin abinda za
faru.....
Mum Twins ?? & Auntie M. Jabo ??
??AN YI WALK'IYA ??
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
K'arfe bakwan safe a gidansu Abeed ta yi mana,
ko da muka shiga gidan suna ta hada_hadar
had'a breakfast, kasancewar ta weekend, Arfat
da Afrat muka hango a kitchen suna ta faman
aiki, tare da 'yan aikin gidan, don mummy ta riga
ta sabar musu da aiki musamman girki don duk
ranar da ba school tare suke shiga kitchen har
Mummy.
Arfat ce ke wanke hannunta a jikin sink, afrat ta
je ta ce da ita
"ya Arfat na ga har yanzu mummy bata fito
ba, ko lafiya "?
Arfat ta ce
"Yanzu nima na ke shirin dubata, ki cigaba
da duba girkin bari na je, na dawo".
Afrat ta ce
"to "
Sallama Arfat ta ke ta kwad'awa tunda ta shiga
parlourn Mummy, har ta K'arasa bedroom,
sannan ta jiyo muryar Mummy tana amsawa
kasa_kasa, da sauri Arfat ta K'arasa kan gadon
ta yaye bargon da Mummym ta kudundune a
ciki, tana fad'in
"Mum lafiya,?"
Cikin raunananniyar murya Mummy ta ce
"lafiya lau"
Arfat ta ce
"Amma shine Mummy ba ki fito ba tun
dazu"?
Mummy ta ce
"jikin ne yau bana Jin dadin sa, amma je ki
ga ni nan zuwa".
Jiki a sanyaye Arfat ta ce
"to mummy sai kin fito,"
tare da Jan k'ofar d'akin. Amma a can k'asan
zuciyarta tana tunanin mai ya samu Mummyn su
don ba ta saba ganinta a irin wannan yanayin
ba.
Bayan sun kammala breakfast ne Daddy ya ce
su zauna dukan su yana da magana, Mummy
kuwa da tun shigowarta, ta kasa sakewa don ko
abincin kirki bata ci ba, haka su Arfat ba su iya
tsayawa sun ci abincin ba kamar yadda suka
saba, saboda don duk sun takura ganin halin da
Mummyn su ke ciki.
Daddy ne ya yi gyaran murya ya fara magana
da cewa "Muhammad!"
Yanayin yadda ya fad'i sunan ya saka
Abeed saurin juyawa ya ce
"Na'am," wadda sautin ta bai fita ba, don ko
Arfat dake zaune kusa da shi bata san ya fad'a
ba.
Daddy ya cigaba da fad'in
"Tunda abin na ka ya zo da haka, ka riga
kasan alkawarin da na yi akan aurenka, kuma
kasan ba zan ta6a warware shi ba, don haka
muka yanke shawara ni da mahaifiyarku akan
za mu had'a aurenka kai da 'yar uwarka
Arfat,......!!!"
Tashin hankali muka gano a idanunsa k'arara,
don kuwa ba Abeed ba har Arfat ta shiga rudani,
don wata zabura ta yi, wadda ta yi dai_dai da
tashin Abeed, hakan ya haddasa gwaruwar
kawunansu, lokaci d'aya suka yi baya, kowa
dafe da kan sa.
Ita kuwa Mummy wasu zafafan hawaye ne, suka
biyo kumatunta, don tasan a rina.
Abeed ne ya yi k'arfin halin cewa
"Dad ban gane mai ka ke nufi ba?, ka
fahimtar da ni, Dad ko ka manta we are the
same blood, if am not wrong, Arfat ita ke bina
fa. sannan nan k'aramar k'anwar mu Afrat".
Arfat kuwa da gudu ta je, ta fad'a jikin Mummy
tana kuka, ta ce
"Mummy ban ga ne abinda Daddy ya ke
fad'a ba, how comes zan auri yayana, the same
Mum & Dad fa, ban ta6a ji ba, ko a lokacin
jahilan farko ba,....!!!"
Wata iriyar tsawa Daddy ya daka mata tare
da cewa
"Me kike nufi?, kin fi ni sanin abinda ya
kamata na yi ne?? "
Mummy ce ta ce
"Alhaji sanin kan ka ne, idan yaran nan suka
ji wannan maganar sai sun dimauce har su kasa
controlling kan su, don haka hak'uri za ka yi abi
komai a hankali."
Mikewa Daddy ya yi tare da nuna Abeed da
hannu ya ce
"Kai ka jawo duk abinda ya faru , don haka
ka shirya d'aukan duk abinda ya biyo baya."
Daga haka bai kuma cewa komai ba ya fice
daga parlourn. Abeed K'arasawa ya yi gurin da
Mummy ke zaune ya ce
"Mum sai yanzu zuciyata ta fara hasko
mun, abinda tun d'azu na kasa ganewa, tabbas
na fuskanci akwai wani B'OYAYYEN AL'AMIRI
(Bebeelo ) da ya shafe mu, amma ba ku sanar
da mu ba, don Allah Mummy ki fad'a mana mai
ya ke shirin faruwa da mu ne"??
Mummy kam ba ta san lokacin da ta rushe da
wani irin kuka ba, dama tun d'azu take rike shi,
gaba d'ayansu rungume Mummym suka yi, suna
rarrashinta ,, duk da Arfat da afrat suma kukan
suke yi.
Arfat ce ta d'ago da kanta ta fara magana cikin
kuka ta ce
"Mummy gaskiyar ya Abeed, don ni kaina na
fara wannan tunanin, ko ma miye Mummy
gwanda ku gaya mana, akan ku bar mu cikin
duhu."
Dakyar mummy ta samu ta tsaida kukan da take
yi, ta ce
"ku yi hak'uri 'ya'yana, za ku ji komai, tunda
har Alhaji ya taso da maganar nan, tabbas na
san zai gaya muku duk abinda ya faru, don haka
ku kara hak'uri zuwa an jima za mu k'ara wani
zaman".
Ba don ransu ya so ba suka amince, kowa ya
tashi ya nufi nasa guri zuciyoyinsu cunkushe da
tunani kala_kala........
Mum Twins ??& Auntie M Jabo ??
[4/11, 2:54 PM] ??AN YI WALK'IYA 16&17
??
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Adaidai k'ofar shiga parlourn su ta tsaya don
daidaita natsuwarta, don kar a gane yanayin da
take ciki, sabida lokacin da zata fito tana ta
gwalli da iyayi, a dole ga matar Abeed, bayan
tasan tana da 'yan adawa don akwai
stepsisters d'in da suke sa'anni, kuma kowacce
ta so ace ita Abeed zai aura, amma sai Abbansu
ya ce hafsat aka ba shi, don haka tasan idan
suka san yadda ta kasance musu da Abeed lallai
za su yi mata dariya, ai kuwa tana shiga
kaitsaye d'akinsu ta wuce, ta fad'a gado sharaf,
tana tunanin mafita don gaskiya tana son Abeed,
domin tasan idan ta yi nasarar aurensa ta more
miji kuma ta tsere sa'a.
Amma da ta tuna kalamansa sai jikinta
ya yi sanyi, wannan shi ake kira ga k'oshi ga
kwanan yunwa.
********
Abeed kuwa bayan ya koma gida, wanka ya yi
sannan ya ci abinci, ya yi shirin kwanciya barci,
a sannan ne yake tariyar abinda ya faru
tsakanin sa da hafsat, tsaki ya ja, sannan ya ce
"idan ban da abun Daddy ta yaya waccen
yarinyar zata had'a kan ta da ni, ai kwata_kwats
ba aji na ba ce" ni da na fison mace natural
beauty, amma ga shi ita duk kyan na ta artificial
ne, amma haka ga ni ta ke yi ta had'u, ba ta san
ni ganinta na ke yi kamar wata horror ba," ya
kuma Jan wani tsakin, tare da rarumo pillown sa
ya k'ak'ume da niyyar fara barci, nan da nan
kuwa ya lula duniyar masu barci, mu kuma mu
ka ja masa k'ofa muka fice daga d'akin.
Kusan 6 weeks da zuwan Abeed gidansu Hafsat,
amma ko da wasa bai kuma lek'awa ba, kullum
da uzirin da ya ke bawa Mummy idan ta yi masa
maganar, har ta gaji ta saka masa ido.
Hafsat kuwa kullum sai ta kirashi, shi kuma ya
yi ta mata wulak'anci da cin fuska, daga k'arshe
ma sai ta daina samunsa, don karya sim card
d'in ya yi , ya chanza wani, don karya layi a
gurin Abeed ba wani abu ba ne, halinsa ne ya
saba haka tuntuni, da ga ya yarinya za ta
takurashi da kira zai chanza wani layin.
Hafsat tun abun baya damunta har ya fara
damunta, don har 'yar rama ta yi, ga shi ta kasa
gayawa kowa maganar har ummansu.........
Auntie M Jabo ??& Maman Twins??AN YI
WALK'IYA 17&18 ??
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
A kwance ta ke a d'aki tana aikin na ta, na
neman mafita, kwatsam ta jiyo muryar babbar
aminiyarta, Safiyya tana kwad'a sallama, a
hanzarce ta mik'e ta rungumeta tana fad'in
k'awata yau a gari? Kamar kin san ina neman ki,
don da gobe na ke sa ran zuwa gidanku".
Murmushi Safiyya ta yi ta ce "kamar da gaske"?
Hafsat ta ce" wallahi da gaske na ke yi, domin
akwai wata muhimmiyyar magana da na ke son
gaya miki ki ba ni shawara".
Safiyya ta ce "ok, to gaya mun ina Jin ki, tunda
ga ni na zo", nan da nan Hafsat ta juyewa
Safiyya abinda ya faru tsakanin ta da Abeed, a
jiyar zuciya Safiyya ta sauke, sannan ta ce
"Hafsat shawara kike so na ba ki ko? Hafsat ta
ce eh"
Safiyya ta cigaba da fad'in "kin san ita gaskiya
d'aya ce tak, kuma d'aci ne da ita, i hope idan
na gaya miki za ki daure ki yi amfani da ita?"
Hafsat ta ce" eh insha'Allah"
Safiyya ta ce "ni a gani na ki hak'ura da Abeed
zai fi, don alamu sun nuna ba ya son ki, kuma
baya muradin zaman aure da ke, to hak'ura da
shi zai fi alkhairi, don gaba na ke jiye miki, ki
manta da duk wani buri da ki ka Sakawa
zuciyarki akan auren Abeed, ki yi watsi da
maganar, ki nemi za6in Allah kawai".
Jinjina na kai kawai Hafsat ke yi, alamum
maganar ta shigeta, ta ce "dama nima zuciya
ta, tana ta mun waswasi akan maganar, amma
tun da yanzu kin haska mun inda na kasa ga ni,
insha'Allah na janye daga yau, dama umman mu
tana ta tambayata akan maganar tana son ji
yadda mu ka yi da Abeed, ina ta mata
hanya_hanya, tunda abun ya kasance haka zan
sanarda da ita na fasa kawai, ta sanar da
Abbanmu, tunda dama ba dole aka mun ba, za6i
aka ba ni".
Safiyya ta ce "gaskiya kam, Allah ya sa hakan
ya zama alkhairi," ameen k'awar kirki Hafsat ta
fad'a tare da mika mata hannu suka tafa su na
dariya.
*****
Yau Daddy tunda ya dawo ya ke zabga fad'a,
mummy ce ta sauko tana fad'in Alhaji lafiya?
tun daga sama na ke jiyo maganar ka, mai ya
faru ne? Daddy ya ce "ni da yaron nan ne
Muhammad, d'azu Alhaji Usman ya ke gaya
mun, wai yarinyar wajensa ta janye maganar
aure tsakaninta da shi, kuma na san ba komai
ya saka ta yi hakan ba, sai dan bak'in hali da ya
ke nuna mata, tunda tun fil'azal ya nuna baya
son aurenta kawai dai tilasta shi mu ka yi".
Mummy ta ce "yi hak'uri Alhaji, bari ya zo, na
tambaye shi yanda suka yi da yarinyar,"
Cikin 6acin rai Daddy ya ce "ba na son Jin
komai daga gare shi, kawai idan ya dawo ki
sanar da shi cewa na yanke hukuncin ba zai
kuma yin wani azumi a gidannan ba, sai a gidan
aurensa, don haka ya shirya kafin azumin nan
mai zuwa za a yi aurensa , gobe_goben nan zan
sanar da shi yarinyar da zan kuma nema masa,
don haka ya yi gaggawar zuwa su shirya kansu".
Daga haka bai kuma cewa komai ba, ya wuce
fuuuu ya haye sama, Mummy kam tsayawa ta yi
baki bud'e, don tasan mutumin na ta, idan ya ce
eh, baya ta6a dawowa ya ce a'a......
Mujee zuwa
Auntie M Jabo ?? & Maman Twins ??
: ??AN YI WALK'IYA 19&20??
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Abeed na dawowa, Mummy ta same shi domin
isar da sak'on Daddy, nan take ta zayyana masa
hukuncin da Daddy ya yanke akan maganar
aurensa, zare dara_daran idanunsa waje ya yi,
tare da fad'in
"Mummy kafin azumi fa kika ce ni duk kun bi
kun saka min ido ga mata nan ba'a tsangamesu
ba saini, tsakani da Allah azumin da bai fi 3
months ba, how comes zan iya aure kafin
lokacin, bayan na san ko yanzu wadda Daddy zai
nema mun ba lallai ta dace da ra'ayina ba,"
Jinjina kai Mummy ta yi tare da fad'in
"Abeed har yanzu ba ka hak'ura da
wannan mummunan k'udirin naka ba ko?, nidai
kan gani nake Ka yi hakuri ka kar6i za6in
mahaifinka ya fiye ma ka."
Abeed ya ce
"Mum ba wai na k'i bin maganar Daddy ba
ne, Noo, ki gane mana, nima fa ya kamata a
duba uzurina a yi mun adalci, don ni ba k'aramin
yaro ba ne, da za a ce bani da hankalin da zan
za6i matar da ta dace da ni, kuma ni ba mace
ba bare a mun auren dole,"
ya had'e hannayensa wuri d'aya, ya cigaba
da fad'in
"please mum ki taimaka ki gayawa Daddy ya
hak'ura da zancen auren nan yanzu, har sai na
samu irin macen da na ke son aura".
Ajiyar zuciya mummy ta sauke, sannan ta ce
"Abeed ka san halin Alhaji sarai, tun da ya
taso da maganar nan, Allah kadai zai hana a yi
aurenka a tsukun lokacin da ya fad'a , ni dai
shawarar da zan ba ka, ka daure ka amince da
abun da mahaifinka ya fad'a".
Ba don ransa ya so ba, ya ce
"to"
saboda ya fuskanci ita ma mummy ta kasa
fuskantar in da ya sa gaba.
K'ofa mummy ta nufa tana fad'in
"Ni dai sai da safe, don har na fara Jin
barci,"
Abeed ya ce.
"Allah ya tashe mu lafiya".
Tunda safe Daddy ya sa aka kira masa Abeed,
nan da nan kuwa ya hau kora masa bayani akan
yarinyar da ya kuma nema masa don sun riga
sun gama magana da mahaifin ta, ya ce
"Muhammad ai kasan Alhaji sulaiman ko"?
Gyd'a kai Abeed ya yi don kaf abokan Daddy ba
wanda bai sa ni ba, Daddy ya cigaba da cewa
"To ya baka babbar 'yar sa, sai ka je ku
daidaita kan ku, shiru Abeed ya yi na dan lokaci,
sannan ya ce "
to tare da mik'ewa ya na fad'in
"Bari na je na yi shirin zuwa office kada na
makara".
Daddy ya ce
"ya yi kyau, Allah ya taimaka", Abeed ya ce
"Ameen" tare da fitowa.
Bayan ya dawo daga office, wannan karon bai
jira Mummy ta yi masa maganar zuwa ganin
yarinyar da aka kuma ba shi ba, ya shiga shirin
zuwa, nan da nan ya fesa wankan shi, ya d'auko
wata dakakkiyar shadda grey colour ya saka, ya
murza hularsa kalar shaddar, ya sha perfumes
masu sanyin k'amshi, ya fito fes da shi, a parlor
su ka had'u da mummy ta kalleshi ta ce
"sai ina kuma"?
Murmushi ya yi wanda bai kai ciki ba, ya ce
"Mummy wurin yarinyar da kuka ba ni
mana"
murmushin Jin dad'i mummy ta yi, ta ce
"yawwa my boy, haka na ke so, Allah ya
kiyaye hanya, Allah kuma ya dawo mun da kai
lafiya,"
ya ce
"Ameen Mum," tare da ficewa daga
parlourn.
Driving ya ke yi, yana sauraren wani cool music,
amma duk da haka zuciyarsa ba ta daina masa
tuk'uk'in da ta ke yi ba, don dai ya fito zancen
nan ne don ya cimma burin da ke zucuyarsa,
lokaci d'aya kuma sai ya saki wani murmushin
Jin dadi don tuna abinda ya k'udire a zuciyarsa,
hakan ya yi dai_dai da k'arasowarsa gidan Alhaji
Sulaiman...
Auntie M Jabo?? & Maman Twins ??
??AN YI WALK'IYA ??
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Horn ya yi mai gadi ya wangale masa gate ya
shige, wannan karon direct parlourn gidan ya
nufa, bayan ya shiga sun gaisa da mutan gidan,
aka ce ya zauna a turo masa yarinyar mai amsa
sunan Teema, gaishe shi ta yi cikin kunya da
ladabi, ba laifi shima ya d'an saki fuskarsa, don
ya ga alamun zata yi hankali, amma duk da haka
natacciyar zuciyarsa na masa hud'ubar tsiya,
don haka nan da nan ya fuske, ya hau zayyana
mata sharuddansa,ita ma ba ta tsaya wani
dogon nazari ba tace da shi dama tana da
wanda take so, don dai babanta ya zo da
maganarsa ne shi yasa ta amince, amma tunda
abun haka ne idan don ita ne ta janye akai
kasuwa, murmushin cin nasara Abeed ya yi, don
dai ya lura ba za a samu matsala ba a wurin
teema ba, don haka cikin wayo da dabara irin na
d'a namiji ya nuna mata, ta sanarda daddynta ya
yi hakuri ya janye maganar auren su, tunda tana
da wanda ta ke so, teema ta ce
"Ba damuwa idan dai Daddy na ne bai da
matsala zai fahimce ni".
Murmushi Abeed ya yi tare da mik'ewa ya ce
"To ni zan ta fi"
teema daga nan zaune ta ce
"Allah ya kiyaye hanya".
Ya ce
"Ameen"
tare da fitowa daga parlorn, cikin nishadi ya ke
driving d'in sa har ya zo gida.
A parlor ya tarar da Mummy a zaune, tana
kallon T.V, ta ce
"welcome back, yarona har ka dawo ke
nan"?
Ya ce
"Eh mummy ba ki yi barci ba ne "?
Tace
"Eh ina nan, ina jiran dawowarka ne, amma
daga ganin alamun fuskar nan ta ka an dace,"
dariya ya to tare da fad'in "i hope so", Mummy
ta ce
"Allah ya sa"
yace
"Ameen "
tare da fad'in
"Mummy bari na je na kwanta, wallahi duk a
gajiye na ke".
Mummy ta ce
"Ai ko ni tashi zan yi, don su Arfat tun d'azu
suka yi barci, nima don na tsaya jiranka ne. "
Yau ta kama asabar daga Daddy har Abeed ba
wanda ya je aiki, suna hutawa a gida, don haka
sai can wajen yamma Alhaji Sulaiman ya yi
tattaki zuwa gidan don sanarda da Daddy halin
da ake ciki game da auren Abeed da teema,
tunda ya gaya masa baya son a dauki wani
dogon lokaci kafin a yi auren.
Bayan sun gama tattaunawarsu a cikin gidan,
suka fito Alhaji Sulaiman ya na cewa
"Alhaji Bashir hakuri za ka yi, kasan komai
nufin Allah ne, Allah bai kaddari matarsa ba ce,
kasan yaran yanzu ba a musu dole, wata k'ila
matarsa tana can wani wuri inda ba a zata ba".
Gyada kai Daddy kawai ya yi, amma a k'asan
zuciyarsa yana tunanin, taurin kai irin na Abeed,
da haka suka yi sallama da Alhaji sulaiman,
Daddy yana shiga gida ya rufe Abeed da fad'a ta
inda yake shiga bata nan yake fita ba, daga
karshe ya kuma tabbatar masa da aurensa yana
nan ba fashi kamar yadda ya fad'a sai dai duk
abinda zai yi ya je ya yi.............
Maman Twins ?? & Auntie M Jabo ??
[4/11, 2:55 PM] ??AN YI WALK'IYA 29_30??
©Mrs Saif & Hauwa M Jabo
®NWA
Abeed ne ya fara rarrashinta, yana cewa ki yi
hak'uri Afrat , komai muk'addari ne duk abinda
kika ga ya faru da bawa to haka Allah ya tsara
masa."
Da haka ya yi ta tausar Afrat da kalamai masu
sanyaya zuciya har suka iso gida.
Washe gari ta kama ranar laraba, a ranar aka
sallame su arfat daga asibiti, don ta warke
sumul sai dan abinda ba'a rasa ba.
Tunda suka dawo gida Arfat ba ta wata doguwar
magana bare hira daga eh sai a'a, hakan da take
yi ba k'aramin tadawa mutanen gidan hankali
yayi ba, musamman mummy da Afrat.
Mummy ce ta shiga d'akin su Arfat don yin
magana da ita, kamar dai yadda ta koma tun
faruwar al'amarin haka ma yanzu mummy ta
tarar da ita a zaune ta na aikin tunanin da ta
saba.
Zama mummy ta yi akan gadon da Arfat ke
zaune, sannan ta janyo ta jikinta, cikin sigar
rarrashi ta fara magana
"haba Arfat yanzu rayuwa ta yiyu a haka???
Duk Kin bi kin chanza, kin daina walwala,, ba
kya son cin abinci, kullum ba ki da aikin da ya
wuce zama a d'aki kina tunani, haba Arfan
mummy why "??
Ta k'arashe maganar tare da shafa kanta.
Hawayen da take ta mak'alewa ne suka samu
damar gangarowa a kumatunta ta ce
"Mummy kun k'i ku gaya mana asalin mu,
kullum idan na yi magana sai ku ce za ku fad'a,
amma har yau shiru ga shi kwanaki sai dad'a ja
suke yi ".
Ajiyar zuciya mummy ta sauke, sannan ta ce
" abinda ya sa ba a gaya muku ba Arfat, ba ma
so ne ki kuma shiga halin da kika shiga a baya,
shi ne kawai ".
Still hawayen ta ke yi ta ce
"mum hakan da kuka yi, shi ya ke barazanar
jefani wani hali, domin mummy yanzu buri na
bai wuce nasan ni wacece ba, daga wani tsatso
muka fito ni da k'anwata, ba ni da wani muradi
da ya wuce hakan, domin Jin ainihin labarin mu
shi zai kwantar mun da hankalina".
Mummy ta ce
"Arfat kin yi alk'awari, idan aka gaya miki za ki
kwanta da hankalinki??
Za kuma ki dawo da walwalarki, ki dawo dai
Arfat da na sa ni da bata yanzu ba, kuma ki
kar6i labarin hannu bibiyu a duk yanda ya zo
miki, kin yi alk'awari???
Arfat ta ce "yes mum, i promise you"
Dad'a rungumeta mummy ta yi, ta ce "yawwa
my lady, haka na ke son ji".
Sannan mummy ta cigaba da fad'in
"to ki kwantar da hankalinki idan Allah ya yarda
Alhaji na dawowa za'a sanarda ku komai".
Murmushi Arfat ta yi, for the first time, tun
faruwar lamarin, ta ce "to mummy na gode".
Murmushin mummy ta maida mata tare da
mik'ewa tsaye ta mik'a wa Arafat hannu alamar
ta mik'o na ta hannun su fito tare a dole Arfat
ta mik'e suka fito daga d'akin, mummy na rik'e
da hannunta har suka fito parlour.
Arfat suka tarar a zaune tana kallo, duk da dai
ita ma idonta ne kawai akan TV amma zuciyarta
ta tafi bulayi, shigowarshi ne ya dawo da ita
duniyar da ta shiga, da murnar ta mik'e tana
fad'in
"ah! Sisto yau an fito kenan???
Mummy ta ce
"hmmm! Ga ta nan na 6a66akota dak'yar "
Mummy ta k'arashe maganar da yin Murmushi.
Afrat ta ce
" Mummy aikam kin kyauta, don yawan zaman
d'akin ita kadai yana k'ara mata damuwa."
Mummy ta ce
"sosai kuwa, bari na je na k'arasa girkin can,
don yamma sai dad'a gabatowa take yi, tun da
dai ku kun yi wa kitchen yaji kwana biyu".
Murmushi suka yi dukan su, tare da cewa
"Mummy za mu dawo ne very soon".
Mummy ta ce
"Allah yasa tare da shigewa kitchen.
Auntie M Jabo ?? & Mum Twins ??
[4/11, 2:55 PM] ??AN YI WALK'IYA 26-28
??
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Daga nan Abeed bai zarce da Arfat ko'ina ba sai
asibitin Dr. Usmam wato family doctor d'in su.
Asibitin mai amsa sunan Apex Clinic da ke
nan cikin nasarawa G.R.A, tun kafin ya k'arasa
asibitin ya kira Dr. Usman ya sanar da shi halin
da ake ciki.
Don haka suna isa doctors suka rufu akan ta,
cikin taimakon Allah ba'a d'auki wani dogon
lokaci ba ta farfad'o.
Mummy kuwa bayan fitar Abeed d'auke da Arfat
, side d'in ta ta nufa da niyyar d'auko mayafi
don ta bisu, sai da bayan ta fito waje sai ta ga
wayam,ba Abeed ba motarsa, hakan ya tabbatar
mata da sun tafi asibiti ne.
Juyawa ta yi gurin da Afrat dake tsaye ta yi
wani zuru-zuru da ita, cikin rashin k'arfin jiki
tace
"Afrat yi sauri d'auko mun key d'in motata
mu tafi".
Afrat tace,
"To"
Tare da komawa cikin gida.
A k'ofar shiga parlour suka had'u da Daddy
shima yana shirin fitowa don zuwa asibitin.
Yace
"Ya dai Afrat, ba ku tafi ba ne"??
Afrat ta ce
"Eh Daddy, yanzu za mu tafi, na shiga ciki
ne, key d'in motar Mummy zan d'auko".
Daddy ya ce
"Waye zai yi driving d'in??
Afrat ta ce
"Mummy ce"
Daddy ya ce
"Bar key d'in mu je a tawa motar kawai".
Waje suka fito in da Mummy ke tsaye, Daddy ya
ce
"Maryam ta yaya za ki yi driving a irin wannan
halin??
Sanin kan ki ne ban fiye son kina driving ba,
bare ki na cikin wannan yanayin, abinda za a yi
ku zo mu je manu driver ya kai mu gaba d'aya
hakan zai fi".
Mummy ta ce
"Shi kenan dama na k'agara na ga halin da
take ciki ne shi yasa".
Murmushi Daddy ya yi, ya ce
"Mummyn yara kenan yanzu za ki ganta
Insha'Allah".
Bayan sun isa asibitin a reception su ka tarar da
Abeed, da sauri Mummy ta k'arasa in da Abeed
ke zaune ta ce
"Abeed ya jikin nata, Allah dai ya sa ta
farfad'o "???
Abeed ya ce
"Mum ki kwantar da hankalinki, Arfat ta
farfad'o tun dazu, don dai an mata allurar barci
ne, da ido biyu za ku tarar da ita".
Gaba d'ayan su suka yi murmushi tare da fad'in
"Alhamdulillah"
Dai_dai lokacin Dr usman ya k'araso wurin yana
fad'in,
"ah! Alhaji har kun k'araso ke nan"??
Daddy ya ce
"Eh Dr. ya aiki "??
Dr usman ya ce
" Alhamdulillah!"
Anan dai duk suka gaisa cikin girmamawa,
sannan ya ce
"Ai za ku iya shiga ku dubata"
Daddy ya ce "ok."
Dr. na gaba suna biye har d'akin da aka kwantar
da Arfat, Mummy da hanzarinta ta k'arasa wurin
gadon da Arfat ke kwance, ta ce
" sannu Arfat " Abeed shima K'arasawa ya yi
wurin, ya ce
"Mum ke nan, barci fa ta ke yi, ki ke ta
faman yi mata sannu".
Murmushi kawai Mummy ta yi, ta cigaba da
kallon Arfat, fuskarta ta yi fayau, har ta d'an
fad'a, ta kuma k'ara haske, sai gashin kan ta da
barbazu ko'ina har ya kusan rufe kyakyawar
fuskarta.
Hannu mummy ta saka ta na tattaro gashin har
ta hade shi gaba d'aya ya yi baya, sai dai ba
ribbon d'in d'aurewa.
Kamar Afrat ta San tunanin da Mummy ta ke yi,
ta ce
"Mummy bari na ciro ribbon d'in kaina sai ki
d'aure mata da shi".
Mummy ta ce
"Yauwa Afrat da kin kyauta kuwa".
Daddy ne ya kalli Mummy ta gefen ido ya yi
murmushi domin har ga Allah ya na k'aunar
matarsa, ko don kyawawan halayenta, domin
mace ce d'aya tak, amma tamkar da d'ubu.
Likitan ne ya yi magana ya ce.
"Ai matsalar ta ta, ba wata babba ba ce,
dan stroke ne ta samu sakamakon razana da ta
yi, sai dai don Allah hajiya a rik'a kiyaye abinda
zai saka ta damuwa don gudun kuma faruwar
haka".
Mummy ta ce
"Insha'Allah Dr. Yanzu zuwa yaushe za a
sallame ta"??
Dr ya ce
"ko gobe ma za a iya sallamar ta"
Mummy ta ce
"Allah ya kai mu"
Suka amsa da ameen.
Daddy ya ce
"Yanzu ya za a yi, za ku koma gida ne ku
shirya ko kuwa??
Don na ga ba ku d'auko ko mai ba".
Mummy ta ce
"Gaskiya ni Alhaji ina nan, sai dai ko ku je da
afrat, ta dawo tare da jummai ko da abinda za
ta yi mana anan".
Kwa6e fuska Afrat ta yi, kamar za ta yi kuka ta
ce
ta ce
"Mummy nima gaskiya ina tare da ku"
Murmushi Daddy ya yi, ya ce
"Mummyn yara ke nan to kin ji abinda 'yar ta
ki ta ce ita ma,saboda haka duk ku taso mu tafi
gaba d'aya kwa dawo daga baya, tunda kun ji
Likita ya ce sai zuwa 8pm ko zata tashi, kun ga
kuma kwa shirya a tsanake, tun da akwai nurses
masu kula da patients".
Mummy ba a son ranta ba ta tashi sai don kar
ta yiwa Daddy musu.
Gaba d'ayan su suka fito da niyyar komawa
gida, har Abeed don dai shima a gajiye ya ke
lik'is don tun farkon faruwar al'amarin baya
samun cikakken barci, don gudun abinda zai je
ya dawo.
Abeed ne ya fara shiga motarsa shi da afrat
suka tafi, sannan Daddy suka shiga ta su, shi da
Mummy manu driver ya ja suka tafi.
Bayan sun fara tafiya ne, Afrat ta juyo da
dubanta zuwa ga Abeed ta ce
"Ni kam bros abinda ya faru yana ba ni
mamaki ba kadan ba, wai ta yaya mummy za su
ce ba su, suka haifemu ba, bayan dai dai da
minti d'aya ban ta6a ganin sun nuna wani abu
da zai nuna ba su suka haifemu ba."
Abeed ya ce
"Ba ke kadai ke mamaki ba Afrat, ni kai na
abin ya yi masifar d'aure mun kai, a ce dukan
ku, ku biyu ba su suka haife ku ba, duk da
cewa, duk wanda ya kalleku ya san ciki d'aya
kuka fito don tsananin kamar ku."
Afrat ta ce
" wallahi bros babban burina yanzu bai wuce
na san su waye suka haife mu ba, kuma na san
ta yadda mu ka zo hannun su mummy.... "
Sai kuma wasu hawaye suka fara saraftu a
fuskarta.......
Auntie M Jabo ?? & Mum Twin??AN YI
WALK'IYA 31_32??
©Mrs Saif & Hauwa M Jabo
®NWA
K'arfe takwas na dare, gaba d'ayan su sun
hallara parlourn Daddy, kamar yadda aka saba
Daddy ne ya fara magana kamar haka
"mummyn ku ta sanar da ni duk abinda ku ke
ciki musamman ma Arfat akan maganar da aka
fara kwanakin baya ba a k'arasheta ba,
sakamakon wasu dalilai, amma bayanin da ta zo
mun da shi yanzu ya nuna bayyana muku ainihin
maganar shi zai samar muku da kwanciyar
hankali a zuciyarku don haka muka yanke
shawarar sanar da ku ainihin labarin iyayenku."
A iya sanin mu iyayenku mutanen kirki ne,
domin duk tsawon shekarun da muka shafe tare
ba mu ga wani mummunan hali a tare da su ba,
asalima ba 'yan nan k'asar ba ne,yan k'asar nijar
ne,Allah ne ya hada mu da su kusan shekaru
ashirin da biyu da suka wuce.
A wancan lokacin ba a wannan unguwar muke
ba, muna wata unguwa da ake kira tarauni, anan
dai cikin birnin kano, wata rana muna zaune ni
da mummyn ku da dare bayan sallar magrib,
wani yaro ya shigo ya ce "wai Ana sallama da ni
a waje".
Na ce "da shi ya ce ganin zuwa, bai dade da fita
kuwa nima na fita.
Sai dai wad'anda na tarar a tsaye a wajen, abin
ya matuk'ar ba ni mamaki, don ban San
fuskokinsu ba, a haka dai na tsaya muka gaisa,
namijin ne ya fara magana cikin hausar sa
wadda ba ta fita sosai, don kana ganin su ka
san buzaye ne, "Alhaji alfarma muka zo nema a
gurinka"
Na ce
"Allah yasa zan iya"
Ya ce
"suna so ne idan da hali su zauna tare da mu,
shi zai riqa yi mana gadi, matarsa kuma zata
rik'a taya hajiya aiki"
Na d'an yi Jim! Na d'an lokaci, sannan na ce
"gaskiya ni ba ni da sha'awar mai gadi, domin a
wancan lokacin arzik'i na bai kai haka ba, ina da
kudi daidai gwargwado, don kusan layin da
muke ba wanda ya kama k'afar arzik'i na.
Anan dai suka hau yi mun magiya, har matar da
suke tare ta matso wurin da nake tsaye, ta
durk'usa ta ce
"don Allah Alhaji ka taimaka mana, don idan
muka bar nan ba musan in da zamu dosa ba,
duk inda muka je gudun mu ake yi, wani wuri
har jifan mu aka yi, aka mana korar kare", ta
k'arashe maganar da sakin kuka mai ban
tausayi.
Har cikin raina na tausaya musu, sai dai tunanin
yadda duniya ta lalace, nake yi ka yi wa mutum
alkhairi ya saka Maka da sharri, tun a wancan
lokacin ma, bare yanzu da komai ya k'ara
ta6ar6arewa.
Duk da wasu ke 6ata wasu, ba duka aka taru
aka zama d'aya ba.
Saboda haka na ce da su
"yanzu ka ga ni ban San ku ba, ban san abinda
ya fito da ku daga gida, ka ga kuwa haka kuram
bana d'auke ku na kai gidana ba".
Ya ce
"Alhaji wallahi mu ba mugaye ba ne, k'addara ce
kawai ta fito da mu daga gida , sakamakon wani
iftila'i da ya faru...
Mu 'yan kasar nijar ne, nijar d'in ma wani
k'ungurimin daji, a nan cikin dajin k'auyen mu
yake, mai suna Salmau , mutanen k'auyen gaba
d'aya ba mu wuce 200 ba, kuma kusan dukanin
mu dangin juna ne, muka taru muka tada k'auye
guda, don ko aure a tsakanin mu ake hadawa.
Wata rana da daddare muna kwance wata iska
mai k'arfi ta taso, kanka ce me, ta fara tuge
mana 'yan bukokin mu,anan fa hankalin mu ya
tashi, nan da nan aka tsuge da wani irin ruwa
mai tsananin k'arfi, a hankali ruwan ya fara
tafiya da mutane, kan wani lokaci kusan rabin
duk ruwa ya tafi da su, wasu kuma ruwan na
Jan su,, suna ihu, ba muda abinda za mu iya
musu, haka muka hak'ura muka kyalesu, don
muma Allah ne ya yi da shan ruwan mu a gaba.
Ko da gari ya waye, wadanda suka tsira ba mu
da yawa, kusan duk an mutu, wasu ma ba a ga
gawawwakinsu ba, ciki kuwa, har da iyayen mu
da sauran 'yan uwan mu na jiki.
To tun daga faruwar al'amarin muka yanke
shawarar barin garin, ni da mai d'akina, amma
mun sha bak'ar wahala kafin mu zo nan Alhaji.
Daddy ya juya ya kalli Arfat da Arfat da tunda
aka fara ba su labarin idon su ke zubar da
hawaye ya ce
"a gaskiya a yanda mahaifinku ya sanarda ni, ba
k'aramar wahala suka sha kafin su k'araso
k'asan nan ba, don ya ce tun daga k'auyen su
har zuwa garin marad'i a k'afa zuka je,
kasancewar a wancan lokacin ba hanyar abin
hawa da zata kai mutum cikin gari, sai keken
shanu, shi kuma duk masu irin aikin haddasu
iftila'in ya shafa.
Sai da suka shafe kusan wata uku da kwanaki
suna tafiya kafin su isa, ga shi ba su da wani
wadataccen guzuri, suka yi ta fama da
matsananciyar yunwa, wani lokacin har da
k'ishi......
Auntie M Jabo ?? & Mum Twins ??
[ ??AN YI WALK'IYA 23-25??
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Mummy na tashi daga nan straight 6angaren
Daddy ta nufa, a zaune ta same shi, ita ma
neman kujera ta yi ta zauna jikin ta duk a mace,
sannan ta ce
"Alhaji yaran can fa suna can duk sun d'aga
hankalinsu akan maganar da suka ji, ya kamata
a musu bayani ko hankalinsu zai kwanta."
Daddy ya ce
"haka ne, dama ai dole a yi musu bayani,
6acin da raina yayi ne na taho ba tare da na
musu bayanin komai ba."
Mummy ta ce
"hakuri za ka yi Alhaji ka san sha'anin yaro",
Daddy ya ce
"Ai shi ke nan, ya wuce, yanzu kin ga lokacin
sallah ya gabato, bari na je masallaci, kafin na
dawo kuma kun yi sallah, sai mu kuma wani
zaman".
Mummy ta ce
"hakan za a yi, bari nima na tashi".
Bayan an idar da sallah, Daddy da Abeed tare
suka dawo daga masallaci, da ganin fuskar
Abeed kasan yana cikin rud'u, Mummy kuwa ita
da su Arfat tuni suma sun idar da ta su sallar,
zaman jiran dawowar Daddy Kawai su ke yi, sai
da suka nemi waje suka zauna, sannan Daddy
ya fara magana.
"D'azu na gaya muku mun yanke shawarar
had'a auren kai Muhammad tare da 'yar uwarka
Arfat! Ba don komai muka yi hakan ba, sai don
sanin akwai aure tsakaninku, tsaftatacce ma
kuwa, wanda Allah (S W A) ya halatta muku".
Tuni fuskar Abeed ta sark'e da ta Arfat, suna
kallon junansu, dukaninsu mun hango tsabagen
mamaki a idanuwansu, Daddy ne ya katse musu
tunani ta hanyar cigaba da magana
"domin kuwa a cikin ku akwai wanda ba mu
muka haifa ba...!!!
Gabansu ne ya tsananta fad'uwa, har afrat dake
gefe tana matsar k'walla, da sauri Arfat ta fad'a
jikin Mummy tana kuka take fad'in Mum don
Allah mu dai kar ku ce ba ku kuka haifemu ba,
don duk duniyar nan ba mu San kowa ba sai ku
Mummy,"
k'arashe maganar tare da sakin wani irin kuka,
rungumeta Mummy ta yi tsam, kamar za'a
k'awata ta ce
"Arfat dama kaf duniyar nan mune iyayenku
kowa yasan haka, kada ma ki yi shakkar haka,
wannan maganar an taso da ita ne kawai don a
warware wata matsalar".
Sai kuma ta juya wurin Daddy tana fad'in
"Alhaji don Allah abar maganan haka, tunda
dai an gaya musu akwai aure a tsakaninsu,
kuma sanin kan su ne ba za mu had'a
haramtaccen Abu ba don son zuciyar mu, shi
yasa tun fil'azal ban so aka bayyana wannan
sirrin ba, don ni a tunani na barin zai fi mana
kwanciyar hankali".
Murmushi Daddy ya yi, ya ce
"Maryam ke nan gwanda da kika ce a
tunaninki, amma maganar gaskiya barin wannan
maganar ba shi ne mafita ba, domin yin hakan
shi zai haddasa tashin tashina a tsakanin su
yaran".
Abeed da tun dazu bai ce komai ba, idan ban da
wulla ido da yakeyi, dak'yar ya kalato wani yawu
ya had'iye a bushashshen mak'ogwaronsa,
sannan ya ce
"Mummy gaskiyar Daddy, don mu kanmu idan
aka fayyace komai sai mun fi samun kwanciyar
hankali".
Jinjina kai mummy ta yi, tare da d'ago da kan
Arfat dake kwance a cinyarta ta ce
"Arfat kin ji abinda d'an uwanki ya fad'a kin
amince a bayyana komai"???
Da k'yar Arfat ta iya d'aga kanta ta nuna alamar
eh, don ita kadai ta san halin da take ciki.
Daddy ne ya cigaba da fad'in
" Gaskiyar magana Arfat da ke da afrat ba
mu, muka haife ku ba.!!!"
Dam! dam!! K'irjin Arfat ya dinga bugawa, sai
kuma ta ji parlourn gaba d'aya yana juya mata,
cikin k'araji ta ce
"Mum kin ji abinda Daddy ke fad'a ko"??
Wai ba ku ka haife........ Sai kuma ta yi dif
sakamakon duhun da taga ya mamaye mata
idanuwa,, nan da nan ta yi baya da niyyar
faduwa.
Da sauri Abeed ya rik'ota ta fad'a jikinsa, sai dai
gaba d'aya babu alamar numfashi tare da ita.
Afrat da gudu ta yi kanta tana fad'in
"sis Arfat don Allah kar ki mutu ki bar ni!
Mummy don Allah ku gaya mata ku ne kuka
haife mu, ta tashi".
Sai kuma ta fashe da wani irin kuka mai ban
tausayi, ita kanta mummy kuka take yi sosai,
cikin kukan ta ce
"Alhaji ka ga abinda na guda ko??
Domin nasan halin Arfat da saka abu a rai,
yanzu wannan maganar zata iya janyo mata
wani ciwon".
Daddy ya ce
"yanzu ba lokacin tsayawa yin wannan
maganar, a yi kokarin ceto rayuwar ta tukun".
Sai ya kalli Abeed ya ce
"Muhammad dubo numbern Dr. Usman, ka
kira ka ce ya zo yanzu ina neman sa".
Abeed ya ce
"Dad ai da d'aukan ta a ka yi kawai aka wuce
da ita asibiti kaitsaye da zai fi, ko da asibitin Dr.
Usman d'in ne, tunda kusa ne, ba nisa sosai."
Daddy ya ce shike nan hakan za a yi, nan da
nan Abeed ya suri Arfat, bai ajiye ta ko'ina ba
sai bayan motarsa, bai jira fitowar su Mummy
ba, ya ja sai asibiti.......
Www.hauwajabo.blogspot.com
Www.jabohauwa.WordPress.com
Auntie M Jabo ?? & Mum Twins ??
[4/11, 8:36 PM] Eve Jabo: ??AN YI WALK'IYA
?? 33 & 34
©Mrs Saif & Hauwa M Jabo
®NWA
Haka suka yi ta fad'i tashi har suka iso garin
Kano.
To bayan ya gama ba ni labarin nima na shigo
na sanarda Mummyn ku, da yake akwai ta da
tausayi nan da nan ta amince, mu ka yanke
shawarar mahaifinku zai rik'a yi mana gadi, ita
kuma ummanku idan Allah ya sauke ta lafiya za
ta rik'a taya Mummyn ku aika_aikacen gida, da
yake ko da suka zo tana d'auke da tsohon cikin
ki, ya nuna Arfat da hannu.
Ba su dade da zuwa ba kuwa, aka haifeki,
yarinya mai kyau da ke, ga farin jini, kusan ko
da yaushe a wurin Mummyn ku kike wuni,
kasancewar ta mai son yara, don haka ba
k'aramin sabo ku ka yi ba.
Ba ki fi 2 years ba ta haifi Afrat , don haka Arfat
sai ta koma hannun Mummy da zama gaba
d'aya.
A kwana a tashi ba wuya, ita ma afrat ta fara
girma sai ta nuna, ta fison zama gurin Mummyn
ku akan gurin ummanku, don wata rana da kuka
take tafiya idan ta zo d'aukanta, Mummyn ku ta
ce ita ma a kyaleta a wurin ta tunda ta fison
nan, ummanku sai dai ta yi murmushi kawai, don
akwaita da kawaici, kuma tana Jin dad'in yadda
Mummyn ku, ke nuna k'aunarta a gare ku.
Haka rayuwan mu ta cigaba da kasancewa har
zuwa ranar, wata juma'a da ba za mu manta da
ita ba, muna kwance misalin k'arfe biyun dare,
wani irin k'auri ya tashe mu, a firgice muka fito
harabar gidan, ai kuwa nan da nan muka hango
wani irin hayak'i yana tashi daga boys quarters ,
ba shiri muka nufi can, ashe wuta ce ta kama,
wadda ba mu san musabbabinta ba har yau,
domin ko da muka je mahaifanku babu mai
sauran numfashi, domin 90% na jikin su duk ya
k'one."
Hawaye ne kawai ke zubowa daga fuskar su
Arfat tare da maimaita Innalillahi
Wa'inna'ilaihirraji'un! Daddy ya cigaba da fad'in
"duk abin nan da ke faruwa Abeed baya nan,
yana k'asar Cyprus don tun yana da 4 years
k'anina ya dage yana so a ba shi Abeed d'in don
ya fara makaranta acan, don akwai makarantar
da yaransa ke yi, da yake shi ya riga ni fara tara
iyali, don wasu daga cikin yaransa duk sun
girmi Abeed.
Bai dawo Nigeria ba, sai da ya gama secondry
school, sai dai mu muna ziyararsa time to time,
kuma tun a wancan lokacin dama an gaya masa
yayi k'anne don har pictures d'in ku ana tura
masa.
So that da ya dawo, ya tafi a zuwan ku
kannensa ne uwa d'aya uba d'aya, don ko
dangina na yi musu kashedin kar wanda ya
sanar da ku, har sai lokacin da muka yanke, don
ko da wannan maganar ba ta taso ba, mun
yanke shawarar gaya muku, idan dai wa'adin da
muka saka ya cika,sai ga shi kuma haka ta faru.
Wanna shine abinda muka sani game da
iyayenku".
Arfat tashi ta yi daga in da take zaune, zuwa
gurin da Mummy da Daddy ke zaune ta fara
magana cikin kuka ta ce
"Mum, Daddy ba mu da bakin da za mu gode
muku, sai abinda na sani bakunan mu baza su
ta6a daina muku addu'ar alkhairi ba, har sai
ranar da numfashinmu ya bar jikin mu, haka
iyayenmu daga yau za mu saka su cikin addu'a
har ranar da Allah zai kar6i rayuwar mu, don
addu'ar mu garesu shi zai sa su yi alfahari da
haihuwar mu".
Na yi matuk'ar farin ciki da suka, zama
iyayenmu, domin babbar fargabata bai wuce a
ce ba mu da iyaye ba, sai ta saki wani
murmushi wanda yayi dai_dai da gangarowar
wasu hawaye masu sanyi a fuskarta ta ce
"Alhamdulillah!
Daddy ne ya kalli gefen da Abeed ke zaune ya
ce
"Muhammad ka ji labarin 'yan uwanka, hope za
ka rik'eta da amana tunda dai ka ji marainiya ce
".
Hmm! Kawai Abeed ya ce tare da mikewa tsaye
yana fad'in
" ni duk na gaji dad, bari na je na d'an kwanta,
na huta".
Bai jira abinda za su ce ba ya wuce abinsa.
Dukansu zuba masa ido suka yi, suna karantar
wani abu a tare da shi, sai dai ba su kai ga
lalubo amsar ba ya wuce.
Yana zuwa d'aki ya zube akan gadonsa, yana
sauke wata naunanniyar ajiyar zuciya, ya d'aga
kan shi sama yana kallon fan, nan da nan ya
Lula duniyar tunani.....
Mum Twins ??& Auntie M Jabo ??
[4/12, 9:00 ??AN YI WALK'IYA ??35_37
©Mrs Saif & Hauwa M Jabo
®NWA
Ya fi k'arfin 1hr a kwance, yana tunani sai dai
ya kasa lalubo mafita, don haka ya mike tare da
sakin tsaki, key d'in motarsa ya d'auka ya yi
waje, daga nan bai zarce ko'ina ba sai gidan su
mubarak.
Ya taki sa'a kuwa ya same shi, mubarak ne ya
fito da murnarsa sai dai yanayin da ya ga abokin
nasa ne ya sa gwiwarsa ta yi sanyi, ya ce
"mutimina ya dai??? Na gan ka wani iri, me ya
faru ne??
Tsaki Abeed ya kuma ja, sannan ya ce
"wallahi wata matsala ce, ta dabaibaye ni, na
rasa ya zan 6ullowa al'amarin gaba d'aya kai na
ya kulle shi yasa, ka ga na zo wurinka, ko akwai
mafitar da za ka nema mun".
Mubarak ya ce
"ina jinka abokina, gaya mun abinda ya faru".
Abeed ya ce
"ai maganar ce, fad'arta ma abun kunya ne, a
gurina don na yadda da kai ne shi yasa ma har
na zo gurinka, amma abun mtsss....... Sai kuma
ya yi shiru yana girgiza kai, Go on, mubarak ya
fad'a, tare da nuna alamar k'aguwa ya ji
zancen.
Abeed ya ce
"tunda na zo ai dole na gaya Maka, nan da nan
ya juyewa mubarak duk abinda ya faru.
Murmushi mubarak ya yi, tare da cewa
"Abeed ai wannan had'in na ku, ya yi wallahi,
mai abun kunya a nan??
Ni da farko da ka fara magana na d'auka wani
mugun abun kunya ka...... Abeed ya katseshi
sakamakon d'aga masa hannu da ya yi ya ce
"ya isa haka, ban saka ka dogon surutu ba, ni
dai kawai na zo ka ba ni shawarar yadda zan
su6ucewa auren ne, ba tare da ran su Daddy ya
6aci ba".
Mubarak ya ce
"Abeed idan dai shawarar kwarai ka ke so, to
kada ka yarda ka bijirewa auren Arfat, don
aurenku ba k'aramin da cewa ya yi ba.
Hannu Abeed ya d'aga masa a zafafe ya ce
"ta ina muka dace??? Tana matsayin 'yar mai
gadi,kuma' yar mai wanke_wanke da shara, ba
dacewa sam a tsakanin mu".
Galala mubarak ya yi, yana kallonsa, ya ce
"Abeed ai wannan sirrin gidan ku ne, ba wanda
zai san da haka, sai dai idan ku kuka fasa kowa
ya ji."
Abeed ya ce
"ta yaya za a ji zan auri k'anwata, ka ce duniya
ba ta tambayi ta yaya haka ya kasance ba,
kuma sanin kan ka ne dole'yan matan da suka yi
haukan so na, su yi mun dariya kuma ajina ya
zube k'asa wanwar, idan an ji, zan aure 'yar
maigadin gidanmu".
Mubarak ya ce
"gaskiya ka yi nisa ba ka Jin kira, amma ni ban
ga aibun wannan auren ba".
K'wafa Abeed ya yi, ya ce
"yayi kyau", daga haka bai kuma cewa komai ba
ya shuri takalminsa ya fice, mubarak yana ta
k'wala masa kira bai saurareshi ba, ya yi gaba.
Arfat kuwa tunda haka ta kasance, ta karbi
za6in da aka musu hannu bibiyu, domin ta yi
alk'awarin yi ma su mummy biyayya matuk'ar
abinda suka sakata bai sa6awa shari'a ba, abu
d'aya ta ke tunani ta yadda za ta kar6i Abeed a
matsayin miji, bayan kallon da ta ke masa na
d'an uwanta shak'ik'i, duk da dai ya hada duk
wani abu da take buk'ata a d'a namiji, murmushi
ta yi, sannan ta lumshe idonta, afrat da ke
gefenta a zaune tana daddanna phone ta ce
"sisto ke da waye ne??
Kike ta faman murmushi "?
Zaro ido Arfat ta yi ta ce yaushe?? Don bata san
ma ta yi ba,, nan da nan afrat ta d'ago ta, ta yi
murmushi ta ce
" share kawai "
Kwanaki sai tafiya suke yi, amma har yanzu
Abeed ya k'i tsayawa ya yi magana d'aya, duk
lokacin da aka taso da zancen aurensu da Arfat
sai yayi ta hanya_hanya.
Har Daddy ya gaji yau ya titsiye shi akan sai ya
gaya masa, mai ya ke nufi ne akan maganar
aurensu.
Daddy ne ke ce da Abeed
"ba ka ji abinda na fad'a ba ne ka yi shiru??
Sosa k'eya Abeed ya hau yi, ya ce
"Wallahi Daddy dama...... Sai kuma ya yi shiru,
Daddy ya ce
"dama me??
Ya cigaba da fad'in
"wai da an ba ni dama na nemi wata, saboda
gaskiya ni.... Sai kuma ya kuma yin shiru, a
zafafe Daddy ya ce
Ka cigaba da magana kar ka 6ata mana lokaci.
Abeed ya cigaba da fad'in
"gaskiya Daddy ba class d'ina ba ce saboda....
Ai bai ka ga K'arasawa ba Daddy ya d'auke shi
da mari, sannan ya nuna shi da hannu ya ce
"ban k'ara tabbatar da ba ka da tunani ba, sai
yau, to wallahi idan kana son ka ga tsantsar
6acin raina ka bijirewa auren nan, don akan
maganar nan zan iya sa6a Maka fiye da yanda
ba ka zato".
Daga haka bai kuma cewa komai ba, ya fice
daga parlourn fuuuu! Mummy ma ta bi bayansa.
Auntie M Jabo ?? & Maman Twins
??AN YI WALK'IYA ??38_40
©Mrs Saif & Hauwa M. Jabo
®NWA
Jiki a sanyaye Arfat ita ma ta mik'e ta nufi
dakin su, Afrat ta bi bayanta, tana rarrashinta,
don ta hango damuwa a idon yayarta ta k'arara.
Ya rage saura Abeed a wurin, yana tunanin me
abin damuwa akan abinda ya fad'a, bayan
gaskiyar abinda ke zuciyarsa ya fad'a, tabbas da
a ce Arfat iyayenta ba su kasance mak'ask'anta
ba, da ba abun da zai hana ya aureta, don tana
da sifofin da yake so macen da zai aura ta
kasance da su,da wannan tunanin ya bar wajen.
2 weeks later, tun daga ranar da Daddy ya
tadawa Abeed maganar, bai kuma ce da shi
k'ala ba har yau, ya zuba masa ido ne kawai
yana jira ya ga ya saduda, ya bada kai bori ya
hau.
Ashe shi bai san Abeed yana can yana shirin
tafiya ba, don har ya yi visa, ya siye ticket na
tafiya k'asar Cyprus, gurin Baffa Abbakar.
Sai tashi suka yi suka ga ba Abeed alamar sa,
da farko sun za ci ya je office ne,sai aka yi ta
kiran phone d'in sa is switched off, don haka
Daddy ya kira office d'in su aka ce rabonsa da
zuwa office, tun shekaran jiya, nan fa hankalin
su mummy ya fara tashi.
Wasa_wasa an doshi kwana uku ko labarin
Abeed, ba su ji ba, duk wanda ke gidan
hankalinsa ya kai k'oluluwar tashi, idan ka cire
Daddy, don shi cewa ya yi duk inda ya je, shi ne
mai dawowa da kansa.
Washe gari sai ga Baffa Abbakar ya kira, yana
shaidawa Daddy Abeed ya zo wurin su, kuma ya
sanar da shi duk abinda ya faru.
Ran Daddy ya yi matuk'ar 6aci don haka ya ce
da Baffa Abbakar duk abinda ya ke yi ya ajiye
ya taso k'eyar Abeed su dawo tare.
Baffa Abbakar ba yanda ya iya,dole ya
amince, don bai isa ya yiwa Daddy musu ba.
Bayan ya gama wayar ne ya zayyanawa Mummy
duk abinda ya faru. Ita ma ta yi mamakin abinda
Abeed ya yi, sai dai yanda ta ga ran Daddy ya
6aci, ta danne na ta mamakin, ta hau ba shi
hak'uri don ta san, in dai ransa ya 6aci irin haka
komai yana iya faruwa.
Yau ta kama asabar, wurin 2pm su Abeed suka
iso, shi da Baffa Abbakar, sun samu kyakkyawar
kulawa daga wurin mummy. Tun wurin la'asar
gidan ya fara cika da 'yan uwan Daddy kai har
da na Mummy, don duk wani d'an uwa na jiki ya
zo, sakamakon gayyatar da Daddy ya musu na
emergency meeting da za a yi after magrib.
Sai wurin magrib Daddy ya dawo, bayan sun yi
sallah gaba d'ayan su sun hallara, har Baffa
Abbakar. Daddy ya fara magana.
"Alhamdulillah! Ba abinda zan ce da Allah sai
godiya, da ya nuna mun wannan ranar da na ke
son sauke wani nauyi da ya rataya, a wuyana
shekara da shekaru, hak'ik'anin gaskiya na ji
dad'in kasancewar ku anan don ku zame mun
shaida akan abinda zan fad'a, sanin kan ku ne
abubuwa da dama sun faru a shekarun baya,
kwanakin baya an warware wani sirri da ya
dad'e a binne, haka ma yau ina tabbatar mu, da
cewa, zan bud'e d'ayan sirrin, duk da dai ku, kun
san komai, amma shi wanda abun ya faru akan
sa bai sa ni ba.
Sai ya juya 6angaren da Abeed ke zaune ya ce
"Muhammad a yau ina bak'in cikin sanar da kai
cewa ba mu muka haifeka ba, hasalima har
maganan da na ke yi yanzu ba musan iyayenka
ba....!!!
Mum Twins ?? & Auntie M Jabo ??
[4/16, 16)4:36 PM] MRS SAIF ???: ??AN YI
WALK'IYA ??41_50
©Mrs Saif & Hauwa M Jabo
®NWA
Tashin hankali wanda hausawa suka ce
"ba'a saka masa rana " don kuwa Tashin
hankalin da muka hango cikin idanun Abeed ba
zai ma misaltu ba, don dara_daran idanunsa sun
k'ank'ance sun yi jajir kamar an zuba kwanon
barkono a ciki,ya jik'e jagab da gummi duk da
sanyin AC da ya game parlourn.
Da kyar ya iya Jan jiki, ya je gurin da Daddy ke
zaune, dafa k'afafuwan Daddy ya yi cikin k'uncin
zuciya ya fara magana, daga ji ka san yana
cikin tsananin rud'ani ya ce
"Daddy don Allah ka yafe mun abun da na yi
maka, kada ka hukunta ni ta haka, idan don
auren Arfat ne Daddy wallahi ina son ta, kuma
zan aureta, amma kar ku ce ba ku kuka haife ni
ba".
Murmushi Daddy ya yi sosai ya ce
"yaro dai yaro ne amma, idan ban da abun ka
Abeed haka kurum, zan k'irk'iri k'arya na fad'a,
har na tara mutane irin haka, ko dai ka dimauce
ne ba ka ga jama'ar da ke wurin nan ba???
To bari ka ji wannan maganar haka take duk
wanda za ka tambaya haka zai gaya ma. Don ni
da Maryam ba mu ta6a haihuwa ba, mun dad'e
muna neman haihuwa, mun yi yawon asibiti gida
da da waje amma Allah bai ba mu ba, duk in da
muka je za a ce da mu, ni lafiya ta kalau,
Maryam ce mai matsala, sai dai ko ita ana sa
ran zata iya haihuwa nan gaba, a haka har muka
share 10yrs da aure shiru, ita kuma ga ta da
masifar son yara, ni kuma tsananin son da na ke
mata ya saka ba zan iya had'ata da wata ba.
Don haka muka yanke shawarar zuwa gidan
marayu, mu d'auko yaro,don ya rik'a debe mana
kewar yara.ko da muka je kuwa mun ci sa'a an
kawo ka, wai an jefar da kai a bayan layi, to
tunda muka d'ora idanmu akan ka Allah ya
jarabe mu da tsananin k'aunarka musamman
Mummyn ku, don kana jariri sosai a lokacin,
bayan mun gama cike_ciken takardun da aka ba
mu, daga nan asibiti muka wuce don duba
lafiyarka, da kuma bawa maryam shawarwari ta
hanyar da zata bi ta samu ingantaccen ruwan
nono, don ta yi k'ememe ta ce ba za ta ba ka,
madara ba, sa dai ta shayar da kai da kanta.
Wannan shi ne takaitaccen labarinka, sai ya
yiwa Mummy nuni da ta mik'awa Abeed
takardar da ke hannunta, kar6ar takardar ya yi
hannu na rawa, yana dubawa, takarda ce ta
yarjejeniyar kar6ar yaro a gidan marayu, duk
dauriya irin na Abeed, sai da ya zubar da
hawaye, don takardar da ke hannunsa sai da ta
jik'e jagab da hawaye.
[4/16, 4:37 PM] MRS SAIF ???:
Duk wanda ke parlourn sai da ya tausaya masa,
ni kaina maman Twins na tausayawa Abeed
matuk'a, juyawa na yi wurin da Jabo ke zaune,
na ce
"gaskiya Jabo Abeed ya ba ni tausayi ba kadan
ba"
Ta ce
"gaskiya nima na tausaya masa, amma ai
gwanda da aka yi WALK'IYA fuskar kowa ta fito
ras.
Na ce
"haka ne kuma fa, kin ga AN YI WALK'IYA mun
gano fuskar Abeed a zahirinta na gaskiya, ba
wancan fuskar da mu ke gani a da ba".
Mun shagala da surutu, ashe Daddy har ya
cigaba da magana, sai tsinkayo muryarsa muka
yi, yana cewa
"don haka ke Arfat, kin ji asalin Abeed, idan kin
amince sai a saka lokacin bikin ku nan ba da
dad'ewa ba, Murmushi Arfat ta yi ta ce
"Daddy kune iyayen mu duk abinda kuka zartar a
gun mu dai-dai ne,"
Murmushi Daddy ya yi ya ce
"Allah ya miki albarka, sannan ya juya gurin
Abeed ya ce
"na dawo gareka, duk da dazu ka ce ka amince,
amma yanzu ina so na k'ara tabbatarwa shin ka
amince kuwa???
Gyda kai Abeed ya yi tare da cewa
"Daddy wallahi na amince"
Daddy ya ce
To, Alhamdulillah! Don haka na yanke shawarar
d'aurin aurenku nan da 4wks, duk wanda ke
parlourn sai da ya washe ba ki, ana fad'in Allah
sanya alkhairi.
Sannan Daddy ya ce
"idan akwai mai son magana ya zo ya yi, an ba
shi dama, kowa ya ce ba shi da magana, sai
Mummy ta ce
"ita akwai abinda za ta ce.
Ta ce "ita Jan hankalinta akan yaran ne, don kar
su ji an ce basu suka haifesu ba, tsiro da wasu
halaye, ko kuma su rik'a jajjanye jikin su, na fiso
ku cigaba da halanyanku kamar yadda muka
saba, kada ku saka wani abu a ranku, mu ne
iyayenku, kowa ya San da haka, don ko yanzu,
ba kowa zai san halin da ake ciki ba, don mun
yadda da danginmu, mutane ne masu rik'e sirri,
da haka na ke mik'a godiya ta a gareku, Allah ya
mai da kowa gida lafiya.
Gaba d'aya aka amsa da ameen.
[4/16, 4:41 PM] MRS SAIF ???:
Kwanaki na tafiya biki na dad'a kusantowa,
amma ango da amarya sai wasan 6uya ake yi,
sukan su Mummy sai shirye_shiryen su ke yi,
Abun ba kama hannun yaro.
Can muka hango amarya Arfat, ta yi hanyar
shiga d'akin angon na ta, da sauri muka bi
bayanta don kar a yi ba mu.
Akan gado ta same shi a kwance, ya yi
rigingine, da sauri ya mike Jin muryarta, tana
sallama, amsa sallamar ya yi, sannan ta nemi
wuri ta zauna, ta ce
"ya Abeed, sai da ya ji wani iri, a ransa don
yadda lafazin sunansa ya fita a bakinta, don
yanzu har ga Allah yana Jin son Arfat har cikin
zuciyarsa, kawai kunyar abinda ya faru ne, ya
saka ya kasa zuwa su fahimci juna.
Itama Arfat ta fuskanci haka, shi yasa ta ajiye
tata kunyar ta zo, sai da ta kuma maimaita
sunansa sannan ya amsa.
Ta ce
"haba ya Abeed kullum mummy sai ta yi zancen
mun k'i mu shirya kanmu ga biki sai kusantowa
ya ke, that's why na zo yanzu, ko dai har yanzu
ban yima ba, ta k'arashe maganar da sigar
zolaya.
Waro ido waje ya yi, ya ce ni na isa, kawai dai
ina tuna abinda ya wuce ne , please Arfat for
give me, I beg you".
Arfat ta ce
"come on, bros ka daina tuna abinda ya wuce,
idan ka na tuna abinda ya wuce baza ka yi
rayuwa mai dad'i ba, ni dama ban rike ka a
raina ba. Murmushi Abeed yayi.
Ya ce
"thanks so much, my everlasting wife"
Ita ma Arfat Murmushin ta yi, sannan suka jero
tare don fitowa daga d'akin, ai kuwa suka yi
kici6is da Afrat za ta wuce, sai ko ta hau tafi
raf! raf!! raf!!!
Tana fad'in mummy don Allah yi sauri ki zo ki
ga mutanen ki.
kai sisto, kin ga yadda kuka yi matuk'ar
dacewa?? Let me give you a snap, sai kuma ta
ce "af! ashe wayar ma yana parlour.
Bari na yi sauri na d'auko phone d'in, sai ta juya
da sauri, dariya suka yi sosai Arfat ta ce
"kai Afrat ba dama, sai mu yi ta jiranta fa take
nufi,Abeed ya ce
"ni kai na sai na ga hoton zai bada meaning,
kawai mu jirata, Jan hannunsa Arfat ta yi, tana
cewa mu je ni dai don ina da abin yi.
A kwana a tashi, ba wuya wurin Allah, ga shi
har an shiga satin bikin su Arfat, tun farkon
satin ake shagali iri_iri, don ayi events kala_kala
wasu ma ba mu ta6a Jin sunan su ba, har kawo
yau da dubun dubatar al'umma suka shaida
daurin auren ABEED & ARFAT akan sadaki 50k.
Dare na yi aka sada amarya da tamfatsetsen
gidanta mai kama da aljannar duniya, k'arfe
goma angon ya shigo da abokansa akayi sayen
baki na alada aka bar ango da Amaryar sa,ya
umurceta da si tashi, suka gabatar da nafila,
sannan ango ya ciyar da amaryarsa, shima ya
ci, suka yi hani'an, sai ga ni muka yi Abeed ya
nufo inda muke la6e ya ce
"don Allah ku fita haka, d'aukan rahoton kuma
ya isa haka, wanda kuka yi a baya ma ya yi yan
sa ido kawai , sai dai mu ce “Allah ya saka da
alkhairi."
Ba shiri muka fito muka yi waje Jabo sai Harare
hararee takeyi, tun daga lokacin ba mu kuma
waiwayarsu ba sai bayan 1yr, ko da muka je
mun tarar da Arfat da katon cikin, haihuwa ko
yau ko gobe.
Daga nan gidan su mummy muka je, don ganin a
wani hali su ke, abin mamaki, sai muka tarar da
mummy da ciki, katoton gaske don har ya fi, na
Arfat girma.
Bayan sati da zuwan mu mummy ta haihu ta
samu babies d'in ta twins, mace da namiji,
kyawawan gaske, washe gari Arfat ta haihu ita
ma, ta samu baby boy, mai kama da Abeed sak,
murna a wurin wannan familyn ba a magana.
Don sadakar da Daddy ya yi Allah kad'ai ya San
iyakarta, don taron sunan ma hadewa aka yi, an
yi k'ayatacciyar walima, don nuna godiar su ga
Allah, don kuwa naira ta yi kuka da Idonta.
4 month letter, Abeed muka hango da shi da
Arfat, a zaune a garden d'in gidansu, suna huta,
shi kuma babynsu mai amsa sunan SULTAN,
(kasancewar sunan Daddy aka saka masa) shi
yasa suke kiransa da SULTAN, yana zaune a
kyakkyawar walker d'in sa.
Arfat ta zuba masa ido tana kallonsa, Abeed ne
ya matso in da take, ya hure mata ido da iskar
bakinsa, sannan ta sauke ajiyar zuciya, ya ce
"babyna wai mai yasa me ki ne???
Tun dazu sai kallon SULTAN kike yi, ko ya
chanza miki ne??
Murmushi ta yi ta ce
"wallahi kawai ina tunanin yanzu yaron nan
mallakin mu ne, sai na ji kamar a mafarki."
Dariya Abeed ya yi sosai ya ce
"wato yanzu wahala ta wuce, sai dadi, a lokacin
da kina labour, har wasiyya kin ba ni, a zaton ki
mutuwa za ki yi.
Ya cigaba da fad'in "Arfat please ko nan gaba ki
daina yawan fad'ar mutuwa, Allah hankalina ya
matukar tashi, idan kin anbaci kalmar mutuwa
akanki, I know mutuwa dole ce, amma yanzu
zuciyata ta gama aminta da ke, ke kad'ai ce
burina, sai babyn mu and wasu kids d'in da na
ke saran za ki haifa mun nan gaba, babu wata
mace da zata kai ki k'ima a idona, it will be an
empty world without you, my everlasting wife".
K'ank'ame shi Arfat ta yi,
Tana fad'in "haba hubbyna na ce kadai na fad'ar
wannan maganar dukan mu fa marayu ne, I give
you my words, bazan ta6a barinka ba matukar
ina numfashi a doron k'asa.
Rungumeta Abeed ya yi tsam a jikin sa, yana
cewa na gode, k'anwata, Allah ya ba mu tsawon
kwana mai amfani tare da zuri'a d'ayyaba, a tare
suka ce ameen, tare da sakin Murmushi.
TAMMAT BIHAMDULILLAH!
Anan muka sauke wannan littafin, muna fatan
Allah ya yafe mana kurakuran da muka yi abisa
rashin sa ni, ko kuma ajizanci na d'an Adam.
Luv u ol our fans ??????
Maman Twins?? da Hauwa M Jabo ke muku
fatan alkhairi ??

          By
HAYATU BABA ZUBAIRU
 
share please
thanks for reading

1 comment: